• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daftarin Sin Ya Samar Wa Kamfanoni Masu Jarin Waje Damammaki Masu Kyau

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Daftarin Sin Ya Samar Wa Kamfanoni Masu Jarin Waje Damammaki Masu Kyau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan gwamnatin kasar Sin ta fitar da daftarin tabbatar da karkon jarin waje na shekarar 2025 a ranar 19 ga wata, masana sun ce, wannan daftari ya bayyana aniyar kasar Sin ta karfafa bude kofa ga waje, da kuma fatan kasar Sin na yin hadin gwiwa da kamfanoni masu jarin waje domin cimma moriyar juna.

Cikin ’yan shekarun nan, kamfanoni masu jarin waje sun gane wa idanunsu manufar bude kofa ga waje ta kasar Sin, inda suka ba da gudummawa tare da cimma moriya. Kasar Sin tana dukufa wajen neman zamanantar da kanta ta hanyar inganta bunkasuwar kasar yadda ya kamata, tana kuma karfafa bude kofa ga waje. Daftarin da gwamnatin kasar ta fidda, za ta ba da gudummawa ga Sin wajen neman zamanantarwa, har ma da samar da damammaki ga kamfanoni masu jarin waje a fannin habaka kasuwanni da neman ci gaba, yayin da kuma zai taimaka musu wajen tunkarar kalubaloli iri-iri, ta yadda za su sami ci gaba cikin hadin gwiwa.

  • Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
  • Dangote Ya Koma Matsayi Na 86 A Jadawalin Masu Arziƙin Duniya

Cikin daftarin, an habaka hanyoyin zuba jari a fannoni daban daban, domin tabbatar da bunkasuwar kamfanoni masu jarin waje a kasar Sin. Ban da haka kuma, an samar da sauki ga kamfanoni masu jarin waje wajen gudanar da ayyukansu a kasar Sin, lamarin da ya taimaka musu a halin yanzu, har ma zai ba da gudummawa ga bunkasuwarsu a nan gaba. Rahoton da kungiyar ’yan kasuwan kasar Amurka dake nan kasar Sin, wato AmCham China ta fidda, ya nuna cewa, a bana, kamfanonin dake shafar harkokin saye da sayarwa kimanin kaso 70 bisa dari, za su zuba karin jari a kasar Sin.

Haka kuma, ana bukatar aiwatar da dukkanin matakan da aka ambata cikin daftarin kafin karshen shekarar 2025. Wannan wata kyakkyawar alama ce da kasar Sin ta samar wa kamfanoni masu jarin waje. An yi imani cewa, sakamakon jerin matakan da kasar Sin ta fidda domin tabbatar da karkon jarin waje, zai tabbatar da ganin kamfanoni masu jarin waje sun hadu da damammaki da dama a kasar Sin, tare da gano karin damammakin inganta kasuwanninsu a kasar. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jirgin Saman Da Kasar Sin Ta Kera Mai Amfani Da Lantarki Ya Yi Tashin Farko Cikin Nasara

Next Post

Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.