• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Asabar 8 Zuwa Talata 11 Ga Watan Muharram 1444

by Ishaq Idris Gulbi
3 years ago
in Rahotonni
0
Gwamnatin Tarayya Ta Ware Biliyan 2.6 Domin Tsaron Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamualaikum barkanmu da asubahin Asabar, takwas ga watan Muharram, shekarar 1444, bayan hijirar cikamakin annabawa kuma fiyayyen halitta, Annabi Muhammad S. A. W. Daidai da shida ga watan Agusta, shekarar 2022.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya amince a kashe wata Naira Biliyan 24, ga aikin noman rani domin bunkasa sana’ar noma.

  • Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan
  • Yadda Mai Wanke-wanke Ta Zama Mataimakiyar Shugaban kasa

An tsaurara tsaro a gidajen yari da ke jihohin Kabbi, da Zamfara da Katsina, don dakile dukkan wani hari da za a iya kai wa gidajen.

Kungiyar gidajen rediyo da talabijin ta kasa BON, ta zargi hukumar kula da gidajen rediyo da talabijin NBC, da yin azarbabi, da saba wa dokar NBC, da rashin adalci, a takardar tarar Naira Miliyan Biyar da ta kai wa gidan talabijin na Trust da wasu kafofin watsa labaru, a kan nuna wani bidiyo na rahoto a kan ‘yan ta’adda.

A jihar Kano ‘yan kwana-kwana sun yi nasarar sauko da wani matashi kasa, da ya makale a gada, ya ce ko Buhari ya sauka daga mulki, ko ya fado kasa daga gadar ya mutu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

A jihar Binuwai, gwamnan jihar Ortom, ya ce zai sayo wa ‘yan bijilanti na jihar bindigogi kirar AK47 don taimaka wa tsaro a jihar.

A Abuja an sace wani dan takaran gwamna na jihar Filato a jam’iyyar LP Yohanna Margif.

A jihar Sakkwato, da yake ‘yan makarantar da aka kashe Deborah za su koma makarantar ranar 8 ga watan nan wato jibi, gwamnatin jihar ta ce daliban za su biya kudi domin gyara kayayyakin da suka barnata.

A jihar Kaduna, ‘yan kungiyar Ansaru ne suke ta aure ‘yan matan yankin Birnin Gwari ana ta shagulgula.

Sai yankin Mando da ake ta korafi a kan badakalar da ake zargin an yi a rabon gidan sauro.

Sai kuma ma’aikatan hukumar yada labaru ta jihar Kaduna KSMC, da aka sallama aiki tun farkon shekarar da ta gabata, ba tare da an ba su ko taro na raba mutum da aikinsa rana tsaka ba, suna ci gaba da godon a biya su hakkokinsu.

A jihar Katsina, masu fashin jama’a da kisa da satar dabbobi ne, suke ci gaba da fashin matan aure da ‘yan mata, da kashe maza da tsofaffi.

LAHADI

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi tir da kisan wulakanci da Inyamurai suke ci gaba da yi wa Hausawa da ke zaune a kasashensu na Inyamurai.
Kungiyar dattawan Arewa ta yi tir da kisan wulakanci da Inyamurai suke ci gaba da yi wa Hausawa da ke zaune a kasashensu na Inyamurai.

Keyamo ya roki iyayen yara, su roki malaman jami’a su bude jami’o’i dalibai su koma aji.

Ya ce gwamnati ba za ta iya ciwo bashin Naira Tirilian 1.1 domin biyan bukatun malaman don kawo karshen yajin aikin da suke kai a yanzun haka ba, saboda ba ta da wannan kudi a yanzun. Kwalejin horar da kananan hafsoshin soja NDA, ta yi wa manhajarta gyara, tare da saitata domin ta iya tinkarar matsalar tsaro ta zamani da bullo wa matsalar ta bayan gida.

Kungiyar mamallaka gidajen rediyo da talabijin na AREWA, NBMOA a takaice, ta bukaci hukumar kula da gidajen rediyo da talabijin ta kasa NBC a takaice, ta janye tarar Naira Miliyan Biyar da ta yi wa gidan talabijin na Tb Trust.

Yahaya Bello na jihar Kogi, ya tsaurara tsaro a jihar a daidai lokacin da wasu ‘yan bindiga, suka kashe Indiyawa biyu, da ‘yan sanda hudu a Ajakuta.

A jihar Taraba, masu fashin jama’a, sun kashe mutum uku, suka sace mutum ashirin da uku, suka korianoma daga gonakinsu.

A jihar Nasarawa, an kama wani akanta, da sitokifa, saboda bacewar takin zamani tirela tara.

A jihar Kaduna, dan takaran gwamna na jihar Kaduna na jam’iyyar PDP Isah Ashiru Kudan, yana yi wa al’umar musulmj na jihar Kaduna da duniya bakidaya, fatan alheri a wannan lokaci na azumin Ashura da Tasua da za a yi yau Lahadi da gobe Litinin, da addu’ar Allah Ya mana maganin matsalolin da kasar nan take ciki.

LITININ

Sojojin sama na Nijeriya sun ce sun yi nasarar gamawa da ‘yan ta’addan nan da suka kai wa ayarin shugaban kasa farmaki a hanyar ayarin ta zuwa Katsina don shirye-shiryen zuwan Buhari yin babbar Sallah da ya yi a Daura.

Kungiyar daliban Nijeriya ta ba gwamnatin tarayya wa’adin kwana bakwai ta sasanta da malaman jami’a, tare da bai wa shugaban kasa shawarar ya kori Adamu Adamu da Ngige.

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta SERAP, ta kai gwamnatin tarayya kara kotu, a kan tarar Naira Miliyan Biyar da ta ci gidan talabjjin na TB trust da sauransu.

Shugabannin ‘yan Nijar mazauna Nijeriya, sun kakkausar suka a kan yadda Inyamurai suke ta kashe ‘yan Nijar da ke zaune a kasashen Inyamurai, har da fille musu kai.

Suka ce a Nijar ba ka isa ka taba lafiyar wani Inyamuri ba, sai ka shiga uku wajen hukuma. Amma sai ga Inyamuri yana kashe ‘yan Nijar har da fille musu kawuna a Nijeriya, kuma hukumomin Nijar sun yi shiru.

Wani bayani yana cewa gaskiya rashin biyan malaman jami’a albashi har tsawon kusan wata shida, ya jefa su cikin mawuyacin hali tare da iyalansu.

A jihar Barno, ‘yan ISWAP sun kashe wasu mayakan Boko Haram su takwas.

A jihar Bauci, gwamnatin jihar ta rada wa jami’arta ta jihar sunan Sa’adu Zungur wato Sa’adu Zungur Unibersity.

A jihar Katsina, masu fashin jama’a sun yi fashin ango da amaryarsa, sannan suka kashe mutum guda.

TALATA

A karshe dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya saki Dariye da Nyame daga gidan yari na Kuje da ke Abuja. Sakamakon karin kudin haraji da Gwamnatin Tarayya ta yi wa kamfanonin sadarwa, kudin kira da na data za su karu da kashi 100.

Hukumar Shirya Jarabawa ta Yammacin Afirka WAEC, ta fitar da sakamakon jarabawarta ta bana/2022, inda kashi 76 cikin kashi 100 da suka rubuta jarabawar suka ci.

Gwamna Ortom na jihar Binuwai, ya rubuta wa shugaban kasa Buhari neman izinin bai wa ‘yan bijilante na jiharsa bindiga don taimaka wa tsaro a jihar.

Ma’aikatan kamfanin raba wutar lantarki wato DISCOs na Kano, sun ba kamfanin wa’adin mako biyu, ko ya saki kudaden da ake cire musu na fansho ga hukumomin fansho, ko su yi yaji.

Kungiyar Malaman jami’a ASUU shiyyar Kano wacce ta kunshi dukkan jami’o’in da ke jihar Kaduna, da Kano, da Jigawa da sauransu, ta kalubalanci gwamnan jihar Kaduna El-Rufai da ke barazanar korar malaman jami’ar jihar Kaduna, ya nuna wani gini guda daya tal, da ya san shi ya gina shi a jami’ar, a shekara kusan takwas da ya yi yana gwamnan jihar Kaduna.

Ta ce Tetfund/asusun tallafa wa ilimi a manyan makarantu wanda ASUU ce ta yi sanadiyyar kafa shi, shi yake ta gine-gine a jami’ar ba El-Rufai ba.

Jiya Litinin, sabon kwanmandan rundunar soja ta daya da ke Kaduna, Manjo Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, ya karbi raganar mulki daga wanda ya gada Manjo Janar Kabir Mukhtar.
Kotu ta sa bakwai ga watan gobe, ta zama ranar sauraron wata kara da aka kai Tinubu, da wanda ya kai karar yake zargin Tinubu ya mika takardun bogi don tsayawa takarar neman shugabancin kasar nan.

Melle Kyari shugaban kamfanin mai na NNPC, ya ce a duk wata, ana sace wa Nijeriya danyen mai na Dala Biliyan Biyu.

A jihar Taraba, masu fashin jama’a sun kashe mutum uku, suka jidi wasu. A jihar Neja, masu fashin jama’a, sun yi fashin mutum uku, suka kashe mutum guda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKanun LabaraiWaiwaye
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

Next Post

Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

1 day ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

5 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

6 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

1 week ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.