• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Asabar 8 Zuwa Talata 11 Ga Watan Muharram 1444

by Ishaq Idris Gulbi
3 years ago
in Rahotonni
0
Gwamnatin Tarayya Ta Ware Biliyan 2.6 Domin Tsaron Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamualaikum barkanmu da asubahin Asabar, takwas ga watan Muharram, shekarar 1444, bayan hijirar cikamakin annabawa kuma fiyayyen halitta, Annabi Muhammad S. A. W. Daidai da shida ga watan Agusta, shekarar 2022.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya amince a kashe wata Naira Biliyan 24, ga aikin noman rani domin bunkasa sana’ar noma.

  • Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan
  • Yadda Mai Wanke-wanke Ta Zama Mataimakiyar Shugaban kasa

An tsaurara tsaro a gidajen yari da ke jihohin Kabbi, da Zamfara da Katsina, don dakile dukkan wani hari da za a iya kai wa gidajen.

Kungiyar gidajen rediyo da talabijin ta kasa BON, ta zargi hukumar kula da gidajen rediyo da talabijin NBC, da yin azarbabi, da saba wa dokar NBC, da rashin adalci, a takardar tarar Naira Miliyan Biyar da ta kai wa gidan talabijin na Trust da wasu kafofin watsa labaru, a kan nuna wani bidiyo na rahoto a kan ‘yan ta’adda.

A jihar Kano ‘yan kwana-kwana sun yi nasarar sauko da wani matashi kasa, da ya makale a gada, ya ce ko Buhari ya sauka daga mulki, ko ya fado kasa daga gadar ya mutu.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A jihar Binuwai, gwamnan jihar Ortom, ya ce zai sayo wa ‘yan bijilanti na jihar bindigogi kirar AK47 don taimaka wa tsaro a jihar.

A Abuja an sace wani dan takaran gwamna na jihar Filato a jam’iyyar LP Yohanna Margif.

A jihar Sakkwato, da yake ‘yan makarantar da aka kashe Deborah za su koma makarantar ranar 8 ga watan nan wato jibi, gwamnatin jihar ta ce daliban za su biya kudi domin gyara kayayyakin da suka barnata.

A jihar Kaduna, ‘yan kungiyar Ansaru ne suke ta aure ‘yan matan yankin Birnin Gwari ana ta shagulgula.

Sai yankin Mando da ake ta korafi a kan badakalar da ake zargin an yi a rabon gidan sauro.

Sai kuma ma’aikatan hukumar yada labaru ta jihar Kaduna KSMC, da aka sallama aiki tun farkon shekarar da ta gabata, ba tare da an ba su ko taro na raba mutum da aikinsa rana tsaka ba, suna ci gaba da godon a biya su hakkokinsu.

A jihar Katsina, masu fashin jama’a da kisa da satar dabbobi ne, suke ci gaba da fashin matan aure da ‘yan mata, da kashe maza da tsofaffi.

LAHADI

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi tir da kisan wulakanci da Inyamurai suke ci gaba da yi wa Hausawa da ke zaune a kasashensu na Inyamurai.
Kungiyar dattawan Arewa ta yi tir da kisan wulakanci da Inyamurai suke ci gaba da yi wa Hausawa da ke zaune a kasashensu na Inyamurai.

Keyamo ya roki iyayen yara, su roki malaman jami’a su bude jami’o’i dalibai su koma aji.

Ya ce gwamnati ba za ta iya ciwo bashin Naira Tirilian 1.1 domin biyan bukatun malaman don kawo karshen yajin aikin da suke kai a yanzun haka ba, saboda ba ta da wannan kudi a yanzun. Kwalejin horar da kananan hafsoshin soja NDA, ta yi wa manhajarta gyara, tare da saitata domin ta iya tinkarar matsalar tsaro ta zamani da bullo wa matsalar ta bayan gida.

Kungiyar mamallaka gidajen rediyo da talabijin na AREWA, NBMOA a takaice, ta bukaci hukumar kula da gidajen rediyo da talabijin ta kasa NBC a takaice, ta janye tarar Naira Miliyan Biyar da ta yi wa gidan talabijin na Tb Trust.

Yahaya Bello na jihar Kogi, ya tsaurara tsaro a jihar a daidai lokacin da wasu ‘yan bindiga, suka kashe Indiyawa biyu, da ‘yan sanda hudu a Ajakuta.

A jihar Taraba, masu fashin jama’a, sun kashe mutum uku, suka sace mutum ashirin da uku, suka korianoma daga gonakinsu.

A jihar Nasarawa, an kama wani akanta, da sitokifa, saboda bacewar takin zamani tirela tara.

A jihar Kaduna, dan takaran gwamna na jihar Kaduna na jam’iyyar PDP Isah Ashiru Kudan, yana yi wa al’umar musulmj na jihar Kaduna da duniya bakidaya, fatan alheri a wannan lokaci na azumin Ashura da Tasua da za a yi yau Lahadi da gobe Litinin, da addu’ar Allah Ya mana maganin matsalolin da kasar nan take ciki.

LITININ

Sojojin sama na Nijeriya sun ce sun yi nasarar gamawa da ‘yan ta’addan nan da suka kai wa ayarin shugaban kasa farmaki a hanyar ayarin ta zuwa Katsina don shirye-shiryen zuwan Buhari yin babbar Sallah da ya yi a Daura.

Kungiyar daliban Nijeriya ta ba gwamnatin tarayya wa’adin kwana bakwai ta sasanta da malaman jami’a, tare da bai wa shugaban kasa shawarar ya kori Adamu Adamu da Ngige.

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta SERAP, ta kai gwamnatin tarayya kara kotu, a kan tarar Naira Miliyan Biyar da ta ci gidan talabjjin na TB trust da sauransu.

Shugabannin ‘yan Nijar mazauna Nijeriya, sun kakkausar suka a kan yadda Inyamurai suke ta kashe ‘yan Nijar da ke zaune a kasashen Inyamurai, har da fille musu kai.

Suka ce a Nijar ba ka isa ka taba lafiyar wani Inyamuri ba, sai ka shiga uku wajen hukuma. Amma sai ga Inyamuri yana kashe ‘yan Nijar har da fille musu kawuna a Nijeriya, kuma hukumomin Nijar sun yi shiru.

Wani bayani yana cewa gaskiya rashin biyan malaman jami’a albashi har tsawon kusan wata shida, ya jefa su cikin mawuyacin hali tare da iyalansu.

A jihar Barno, ‘yan ISWAP sun kashe wasu mayakan Boko Haram su takwas.

A jihar Bauci, gwamnatin jihar ta rada wa jami’arta ta jihar sunan Sa’adu Zungur wato Sa’adu Zungur Unibersity.

A jihar Katsina, masu fashin jama’a sun yi fashin ango da amaryarsa, sannan suka kashe mutum guda.

TALATA

A karshe dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya saki Dariye da Nyame daga gidan yari na Kuje da ke Abuja. Sakamakon karin kudin haraji da Gwamnatin Tarayya ta yi wa kamfanonin sadarwa, kudin kira da na data za su karu da kashi 100.

Hukumar Shirya Jarabawa ta Yammacin Afirka WAEC, ta fitar da sakamakon jarabawarta ta bana/2022, inda kashi 76 cikin kashi 100 da suka rubuta jarabawar suka ci.

Gwamna Ortom na jihar Binuwai, ya rubuta wa shugaban kasa Buhari neman izinin bai wa ‘yan bijilante na jiharsa bindiga don taimaka wa tsaro a jihar.

Ma’aikatan kamfanin raba wutar lantarki wato DISCOs na Kano, sun ba kamfanin wa’adin mako biyu, ko ya saki kudaden da ake cire musu na fansho ga hukumomin fansho, ko su yi yaji.

Kungiyar Malaman jami’a ASUU shiyyar Kano wacce ta kunshi dukkan jami’o’in da ke jihar Kaduna, da Kano, da Jigawa da sauransu, ta kalubalanci gwamnan jihar Kaduna El-Rufai da ke barazanar korar malaman jami’ar jihar Kaduna, ya nuna wani gini guda daya tal, da ya san shi ya gina shi a jami’ar, a shekara kusan takwas da ya yi yana gwamnan jihar Kaduna.

Ta ce Tetfund/asusun tallafa wa ilimi a manyan makarantu wanda ASUU ce ta yi sanadiyyar kafa shi, shi yake ta gine-gine a jami’ar ba El-Rufai ba.

Jiya Litinin, sabon kwanmandan rundunar soja ta daya da ke Kaduna, Manjo Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, ya karbi raganar mulki daga wanda ya gada Manjo Janar Kabir Mukhtar.
Kotu ta sa bakwai ga watan gobe, ta zama ranar sauraron wata kara da aka kai Tinubu, da wanda ya kai karar yake zargin Tinubu ya mika takardun bogi don tsayawa takarar neman shugabancin kasar nan.

Melle Kyari shugaban kamfanin mai na NNPC, ya ce a duk wata, ana sace wa Nijeriya danyen mai na Dala Biliyan Biyu.

A jihar Taraba, masu fashin jama’a sun kashe mutum uku, suka jidi wasu. A jihar Neja, masu fashin jama’a, sun yi fashin mutum uku, suka kashe mutum guda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKanun LabaraiWaiwaye
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

Next Post

Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Asabar
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.