• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

by Rabilu Sanusi Bena
9 months ago
Benci

A ‘yan shekarun nan, idan aka tambayi wani mai sha’awar kallon fina-finan Hausa cewa, wane jarumi ne idan ya fito a matsayin mara tausayi abin ya fi dacewa da shi a Masana’antar Kannywood? nan take zai ce; Abubakar Waziri ko Baban Ma’u.

Asalin sunan Abubakar Waziri, Garba Muhammad; haifaffen Samaru a garin Zariya da ke Jihar Kaduna. Waziri ya bayyana da kansa cewa, shi mazaunin babban birnin tarayya; Abuja ne. Wata rana masu shirya fina-finai, sun tafi Abuja xaukar wani shirin fim; sai suka buƙaci ya fito a matsayin xan cikon benci a shirin nasu.

  • Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja
  • Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Haka kuwa aka yi, Waziri ya fara a matsayin xan cikon benci, bayan rawar da ya taka a wannan shirin; sai masu shirya fina-finan suka gano akwai baiwar da ke tattare da shi a harkar ta fim, sai suka ci gaba da ba shi ayyuka, in ji shi.

Zuwa yanzu, jarumin ya fito a cikin manyan fina-finan da suka samu tagomashin masu kallo a Masana’antar Kannywood, daga cikinsu akwai; Allah Ya Hana Babu, Kisan Gilla, Labarina, Garwashi da kuma Manyan Mata, wanda dukkanninsu ya taka rawar gani a ciki; ta hanyar fitowa a matsayin wani mara imani ko rashin tausayi.

Dangane da yadda mutane ke xaukarsa a matsayin mugu a zahiri, Waziri ya ce ko alama shi ba mugun mutum ba ne, kawai dai aikinsa ne a haka kuma dole ya zage damtse wajen yin aiki tukuru a duk lokacin da ya samu kansa a cikin shirin fim.

LABARAI MASU NASABA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Ya ƙara da cewa; “Wani lokaci, na tava haxuwa da wani mutum; sai ya buxa baki ya ce, Allah ya tsine maka albarka; sai na ce da shi malam, wannan magana taka ta yi tsauri sosai; domin kuwa ya kamata ka san cewa, yadda nake a fim ba haka nake a zahiri ba. Kazalika, yarana sun tava dawowa daga makaranta suka ce ana ce musu ‘ya’yan mugu; sai na ce musu kada ku damu da maganganun mutane, ku kyale su kawai.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Next Post
Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.