• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

by Rabilu Sanusi Bena
10 months ago
Benci

A ‘yan shekarun nan, idan aka tambayi wani mai sha’awar kallon fina-finan Hausa cewa, wane jarumi ne idan ya fito a matsayin mara tausayi abin ya fi dacewa da shi a Masana’antar Kannywood? nan take zai ce; Abubakar Waziri ko Baban Ma’u.

Asalin sunan Abubakar Waziri, Garba Muhammad; haifaffen Samaru a garin Zariya da ke Jihar Kaduna. Waziri ya bayyana da kansa cewa, shi mazaunin babban birnin tarayya; Abuja ne. Wata rana masu shirya fina-finai, sun tafi Abuja xaukar wani shirin fim; sai suka buƙaci ya fito a matsayin xan cikon benci a shirin nasu.

  • Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja
  • Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Haka kuwa aka yi, Waziri ya fara a matsayin xan cikon benci, bayan rawar da ya taka a wannan shirin; sai masu shirya fina-finan suka gano akwai baiwar da ke tattare da shi a harkar ta fim, sai suka ci gaba da ba shi ayyuka, in ji shi.

Zuwa yanzu, jarumin ya fito a cikin manyan fina-finan da suka samu tagomashin masu kallo a Masana’antar Kannywood, daga cikinsu akwai; Allah Ya Hana Babu, Kisan Gilla, Labarina, Garwashi da kuma Manyan Mata, wanda dukkanninsu ya taka rawar gani a ciki; ta hanyar fitowa a matsayin wani mara imani ko rashin tausayi.

Dangane da yadda mutane ke xaukarsa a matsayin mugu a zahiri, Waziri ya ce ko alama shi ba mugun mutum ba ne, kawai dai aikinsa ne a haka kuma dole ya zage damtse wajen yin aiki tukuru a duk lokacin da ya samu kansa a cikin shirin fim.

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Ya ƙara da cewa; “Wani lokaci, na tava haxuwa da wani mutum; sai ya buxa baki ya ce, Allah ya tsine maka albarka; sai na ce da shi malam, wannan magana taka ta yi tsauri sosai; domin kuwa ya kamata ka san cewa, yadda nake a fim ba haka nake a zahiri ba. Kazalika, yarana sun tava dawowa daga makaranta suka ce ana ce musu ‘ya’yan mugu; sai na ce musu kada ku damu da maganganun mutane, ku kyale su kawai.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
Nishadi

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Nishadi

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Next Post
Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

LABARAI MASU NASABA

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025
Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

Xi Ya Taya Ouattara Murnar Sake Lashe Zaben Shugaban Cote D’Ivoire

November 10, 2025
Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

Rundunar Sojin Sama Ta Kai Hari Kan ISWAP Da Ƴan Bindiga A Borno, Kwara Da Katsina

November 10, 2025
Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

Xi Ya Halarci Bikin Bude Gasar Wasanni Ta Sin Karo Na 15 A Guangzhou

November 10, 2025
Kaduna

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.