• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri

by Rabilu Sanusi Bena
8 months ago
in Nishadi
0
Daga Cikon Benci Zuwa Cikakken Jarumin Kannywood – Abubakar Waziri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan shekarun nan, idan aka tambayi wani mai sha’awar kallon fina-finan Hausa cewa, wane jarumi ne idan ya fito a matsayin mara tausayi abin ya fi dacewa da shi a Masana’antar Kannywood? nan take zai ce; Abubakar Waziri ko Baban Ma’u.

Asalin sunan Abubakar Waziri, Garba Muhammad; haifaffen Samaru a garin Zariya da ke Jihar Kaduna. Waziri ya bayyana da kansa cewa, shi mazaunin babban birnin tarayya; Abuja ne. Wata rana masu shirya fina-finai, sun tafi Abuja xaukar wani shirin fim; sai suka buƙaci ya fito a matsayin xan cikon benci a shirin nasu.

  • Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja
  • Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Haka kuwa aka yi, Waziri ya fara a matsayin xan cikon benci, bayan rawar da ya taka a wannan shirin; sai masu shirya fina-finan suka gano akwai baiwar da ke tattare da shi a harkar ta fim, sai suka ci gaba da ba shi ayyuka, in ji shi.

Zuwa yanzu, jarumin ya fito a cikin manyan fina-finan da suka samu tagomashin masu kallo a Masana’antar Kannywood, daga cikinsu akwai; Allah Ya Hana Babu, Kisan Gilla, Labarina, Garwashi da kuma Manyan Mata, wanda dukkanninsu ya taka rawar gani a ciki; ta hanyar fitowa a matsayin wani mara imani ko rashin tausayi.

Dangane da yadda mutane ke xaukarsa a matsayin mugu a zahiri, Waziri ya ce ko alama shi ba mugun mutum ba ne, kawai dai aikinsa ne a haka kuma dole ya zage damtse wajen yin aiki tukuru a duk lokacin da ya samu kansa a cikin shirin fim.

Labarai Masu Nasaba

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Ya ƙara da cewa; “Wani lokaci, na tava haxuwa da wani mutum; sai ya buxa baki ya ce, Allah ya tsine maka albarka; sai na ce da shi malam, wannan magana taka ta yi tsauri sosai; domin kuwa ya kamata ka san cewa, yadda nake a fim ba haka nake a zahiri ba. Kazalika, yarana sun tava dawowa daga makaranta suka ce ana ce musu ‘ya’yan mugu; sai na ce musu kada ku damu da maganganun mutane, ku kyale su kawai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Zamfara Ya Jajanta Wa Iyalan Da Harin Jirgin Sojoji Ya Rutsa Da Su

Next Post

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

Related

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

14 hours ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

6 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

4 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Next Post
Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

Yadda Za Ki Gyara Mamanki A Sauƙaƙe

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.