• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Dajin Kajurun Kaduna ‘Yan Bindiga Ke Zuwa Su Addabe Mu – Mazauna Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Daga Dajin Kajurun Kaduna ‘Yan Bindiga Ke Zuwa Su Addabe Mu – Mazauna Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Yayin da ‘yan ta’addan da ke addabar Babban Birnin Tarayya da jihohin Kaduna, Nasarawa da Neja ke kara karfi, rahotanni sun cewa ‘yan bindigar sun yi sansani a dajin Kajuru da ke yankin Kudancin Kaduna a Jihar ta Kaduna.

Majiyar tsaro ta bayyana cewa dajin da sojoji ke amfani da shi wajen horar da ma’aikatansu, an yi watsi da su, wanda hakan ya sa ya zama mafakar ‘yan ta’addan.

  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Sa ido Kan Tsaro A Hanyar Abuja Zuwa Kaduna

Kamar yadda PUNCH ta ruwaito, wata majiya ta ce “Yanzu haka masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifukan da ke ta’addanci a Babban Birnin Tarayya sun yi sansani a dajin Kajuru. Kajuru shalkwatar Karamar Hukumar Kajuru ce ta Jihar Kaduna. Dajin ya zama mafakar ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

“Hakika, sojoji sun kashe tare da kama dimbin wadannan ’yan ta’adda a yankin a baya. Amma duk da yadda ake kama su, sai su koma wancan dajin tun da sojoji sun yi watsi da sansaninsu a garin.”

Majiyar ta kara da cewa, “Kisan gilla da yawa ya tilasta wa sojoji kafa sansanin wucin gadi a can, inda suke tsara dabarun fatattakar ’yan ta’addan kuma a zahiri abin ya yi wa jama’a kyau. Amma tun bayan tafiyarsu babu zaman lafiya a yankin, ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da ‘yan fashi sun mamaye yankin.

Hakan na faruwa ne yayin da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya da ke aiki tare da rundunar ‘yansanda ta kasa (NPF), ta kame hanyoyin sadarwar ‘yan bindigar, inda ta bai wa ‘yansanda damar sanya ido kan hirarsu da motsinsu.

“Har ila yau, ’yansanda sun san inda ’yan fashin suke, yadda suke sadarwa, da kuma yadda suke yawo. Suna amfani da wayoyin wadanda suka sace. Suna binne wayoyin a cikin kasa kuma suna yin nisa daga wurin, sannan su dawo don tono wayar kuma suna yin waya a duk lokacin da suke son yin magana da dangin wadanda suka sace don neman kudin fansa.

“Kwana biyu kacal da kaddamar da runduna ta musamman a Abuja da IG, IRT ta kama wasu ‘yan bindiga biyu da wasu da ake zargi da yin garkuwa da mutane su hudu, wadanda ke addabar Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma al’ummomin da ke makwabtaka da su. “Har yanzu ana ci gaba da gudanar da ayyuka.” In ji majiyar.

A ranar Alhamis ta makon jiya, masu garkuwa da mutane sun kai farmaki a Kurudu da ke Abuja, a wani rukunin gidan sojoji inda suka yi awon gaba da wasu mutum uku da suka hada da matar aure da kuma surukin wani lauya, Cyril Adikwu.

Wani mazaunin garin wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa wannan ne karon farko da aka yi garkuwa da mutane a gidan.

Ya ce, “Masu garkuwa da mutane sun kai hari a yankin da misalin karfe 9 na daren. Muna tsammanin mutum biyu ne kawai aka sace, amma daga baya hukumomin kula da gidaje sun tabbatar da cewa mutanen da aka sace su uku ne. Wadanda abin ya shafa dai matar lauya ce da surukinsa, da kuma wani mutum daya, wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba. Harin ya ban tsoro saboda muna jin cewa muna cikin aminci a nan.

“Kamar yadda kuke gani, sojoji su zo nan daga shalkwatarsu. Sun kasance a nan tun lokacin da labarin ya bayyana, kuma sun toshe duk wata hanyar shiga gidan suna bincike a ko’ina. Ba wanda zai iya shiga sai in kai mazaunin gidan ne, kuma za a duba ka sosai.”

Wani mazaunin garin, Austine John, wanda ya zanta da manema labarai, ya bayyana cewa Adikwu ya yi nasarar tserewa. Lamarin ya fara ne da misalin karfe 10 na dare a lokacin da nan muka fara jin karar harbe-harbe, muka gane cewa akwai matsala. Na fita da sauri don ganin ko an kulle gate dina.

“Sai muka ji karar harbe-harbe a gidan Barista, daga nan ne muka sanar da mahukuntan gidan, inda nan take suka fara aiki. Cikin kankanin lokaci sojoji suka zagaya su ma suka fara harbe-harbe, amma kafin su zo, masu garkuwa da mutanen sun tafi da matar da kuma surukin Barista.

An cafke gawurtaccen mai garkuwa da mutane

Rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna ta mika wani mutum da ta yi ikirarin cewa shi ne mai garkuwa da mutane a Abuja, Phillip Chinaza ga rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ce an kama Chinaza ne a Kaduna ranar Alhamis ta makon jiya lokacin da suke tserewa da wani mutum mai suna Segun Akinyemi daga Abuja zuwa Jihar Kano.

Hassan ya ce, “Jami’an, sun tare wata mota kirar Toyota Hilud mai launin toka mai lamba Abuja RBC 90 DC, dauke da fasinjoji hudu ciki har da direban, wadanda ake zargin motar ce ta kai masu garkuwa da mutanen.

“Da aka gane akwai matsala da kuma kokarin tserewa da suka yi, sai daya daga cikin masu garkuwa da mutanen ya harbi ‘yansandan, kuma suka mayar da martani.

A sakamakon fafatawar da aka yi da bindiga, an kubutar da wanda aka sace, Segun Akinyemi da ke zaune a gida mai lamba 10, Flat 2, FCDA Kuarters, Area 3, Garki, Abuja, daya daga cikin masu garkuwa da mutanen kuma, mai suna Chinaza Philip na Life Camp, mai shekaru 28. Abuja, shi ma an kama shi.”

Sojojin Sama sun hallaka gawurtaccen dan fashin daji

Rundunar sojin saman Nijeriya ta yi karin haske kan yadda ta ce dakarunta suka kashe wani kasurgumin dan bindiga mai suna Janari, da mabiyansa da dama a wani sumame da suka kai karkarshin rundunar tabbatar da tsaro ta Operation WHIRL.

Rundunar ta bayyana cewa ta yi nasarar kawar da dan bindigan ne yayin da yake tattara mukarrabansa da niyyar kai hari a Karamar Hukumar Igabi da ke Jihar Kaduna.

Kakakin Rundunar, Air Bice Marshal Edward Gabkwet ya shaida wa BBC cewa rundunar ta sami nasarar ne bayan ta dauki lokaci tana dakon gungun ‘yan bindigar kafin su yi dace su yi arangama da su a yankin Gadar Katako da ke Karamar Hukumar Igabi.

‘Lamarin ya auku ne a ranar 18 ga watan Janairu, amma sai bayan ‘yan kwanaki muka sami tabbacin cewa an kashe wannan dan bindiga da mabiyansa. Shi wannan mutumin Janari mun sami labarin cewa yana da hannu cikin harin da aka kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna’, kuma muna da tabbacin cewa yana da hannu a cikin hare-haren da ake kaiwa a hanyar Abuja zuwa Kaduna,’ in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fintiri Ya Nada Sabbin Manyan Sakatarorin Gwamnati 13

Next Post

Maido Da Huldar Diflomasiya Tsakanin Sin Da Nauru Ya Sake Tabbatar Da Matsaya Guda Uku Da Kasashen Duniya Suka Cimma

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

51 minutes ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

2 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

3 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

8 hours ago
Kaduna
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

9 hours ago
Next Post
nauru

Maido Da Huldar Diflomasiya Tsakanin Sin Da Nauru Ya Sake Tabbatar Da Matsaya Guda Uku Da Kasashen Duniya Suka Cimma

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.