ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Dajin Kajurun Kaduna ‘Yan Bindiga Ke Zuwa Su Addabe Mu – Mazauna Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kaduna

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yayin da ‘yan ta’addan da ke addabar Babban Birnin Tarayya da jihohin Kaduna, Nasarawa da Neja ke kara karfi, rahotanni sun cewa ‘yan bindigar sun yi sansani a dajin Kajuru da ke yankin Kudancin Kaduna a Jihar ta Kaduna.

Majiyar tsaro ta bayyana cewa dajin da sojoji ke amfani da shi wajen horar da ma’aikatansu, an yi watsi da su, wanda hakan ya sa ya zama mafakar ‘yan ta’addan.

  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Sa ido Kan Tsaro A Hanyar Abuja Zuwa Kaduna

Kamar yadda PUNCH ta ruwaito, wata majiya ta ce “Yanzu haka masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifukan da ke ta’addanci a Babban Birnin Tarayya sun yi sansani a dajin Kajuru. Kajuru shalkwatar Karamar Hukumar Kajuru ce ta Jihar Kaduna. Dajin ya zama mafakar ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

“Hakika, sojoji sun kashe tare da kama dimbin wadannan ’yan ta’adda a yankin a baya. Amma duk da yadda ake kama su, sai su koma wancan dajin tun da sojoji sun yi watsi da sansaninsu a garin.”

Majiyar ta kara da cewa, “Kisan gilla da yawa ya tilasta wa sojoji kafa sansanin wucin gadi a can, inda suke tsara dabarun fatattakar ’yan ta’addan kuma a zahiri abin ya yi wa jama’a kyau. Amma tun bayan tafiyarsu babu zaman lafiya a yankin, ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da ‘yan fashi sun mamaye yankin.

Hakan na faruwa ne yayin da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya da ke aiki tare da rundunar ‘yansanda ta kasa (NPF), ta kame hanyoyin sadarwar ‘yan bindigar, inda ta bai wa ‘yansanda damar sanya ido kan hirarsu da motsinsu.

“Har ila yau, ’yansanda sun san inda ’yan fashin suke, yadda suke sadarwa, da kuma yadda suke yawo. Suna amfani da wayoyin wadanda suka sace. Suna binne wayoyin a cikin kasa kuma suna yin nisa daga wurin, sannan su dawo don tono wayar kuma suna yin waya a duk lokacin da suke son yin magana da dangin wadanda suka sace don neman kudin fansa.

“Kwana biyu kacal da kaddamar da runduna ta musamman a Abuja da IG, IRT ta kama wasu ‘yan bindiga biyu da wasu da ake zargi da yin garkuwa da mutane su hudu, wadanda ke addabar Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma al’ummomin da ke makwabtaka da su. “Har yanzu ana ci gaba da gudanar da ayyuka.” In ji majiyar.

A ranar Alhamis ta makon jiya, masu garkuwa da mutane sun kai farmaki a Kurudu da ke Abuja, a wani rukunin gidan sojoji inda suka yi awon gaba da wasu mutum uku da suka hada da matar aure da kuma surukin wani lauya, Cyril Adikwu.

Wani mazaunin garin wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa wannan ne karon farko da aka yi garkuwa da mutane a gidan.

Ya ce, “Masu garkuwa da mutane sun kai hari a yankin da misalin karfe 9 na daren. Muna tsammanin mutum biyu ne kawai aka sace, amma daga baya hukumomin kula da gidaje sun tabbatar da cewa mutanen da aka sace su uku ne. Wadanda abin ya shafa dai matar lauya ce da surukinsa, da kuma wani mutum daya, wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba. Harin ya ban tsoro saboda muna jin cewa muna cikin aminci a nan.

“Kamar yadda kuke gani, sojoji su zo nan daga shalkwatarsu. Sun kasance a nan tun lokacin da labarin ya bayyana, kuma sun toshe duk wata hanyar shiga gidan suna bincike a ko’ina. Ba wanda zai iya shiga sai in kai mazaunin gidan ne, kuma za a duba ka sosai.”

Wani mazaunin garin, Austine John, wanda ya zanta da manema labarai, ya bayyana cewa Adikwu ya yi nasarar tserewa. Lamarin ya fara ne da misalin karfe 10 na dare a lokacin da nan muka fara jin karar harbe-harbe, muka gane cewa akwai matsala. Na fita da sauri don ganin ko an kulle gate dina.

“Sai muka ji karar harbe-harbe a gidan Barista, daga nan ne muka sanar da mahukuntan gidan, inda nan take suka fara aiki. Cikin kankanin lokaci sojoji suka zagaya su ma suka fara harbe-harbe, amma kafin su zo, masu garkuwa da mutanen sun tafi da matar da kuma surukin Barista.

An cafke gawurtaccen mai garkuwa da mutane

Rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna ta mika wani mutum da ta yi ikirarin cewa shi ne mai garkuwa da mutane a Abuja, Phillip Chinaza ga rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ce an kama Chinaza ne a Kaduna ranar Alhamis ta makon jiya lokacin da suke tserewa da wani mutum mai suna Segun Akinyemi daga Abuja zuwa Jihar Kano.

Hassan ya ce, “Jami’an, sun tare wata mota kirar Toyota Hilud mai launin toka mai lamba Abuja RBC 90 DC, dauke da fasinjoji hudu ciki har da direban, wadanda ake zargin motar ce ta kai masu garkuwa da mutanen.

“Da aka gane akwai matsala da kuma kokarin tserewa da suka yi, sai daya daga cikin masu garkuwa da mutanen ya harbi ‘yansandan, kuma suka mayar da martani.

A sakamakon fafatawar da aka yi da bindiga, an kubutar da wanda aka sace, Segun Akinyemi da ke zaune a gida mai lamba 10, Flat 2, FCDA Kuarters, Area 3, Garki, Abuja, daya daga cikin masu garkuwa da mutanen kuma, mai suna Chinaza Philip na Life Camp, mai shekaru 28. Abuja, shi ma an kama shi.”

Sojojin Sama sun hallaka gawurtaccen dan fashin daji

Rundunar sojin saman Nijeriya ta yi karin haske kan yadda ta ce dakarunta suka kashe wani kasurgumin dan bindiga mai suna Janari, da mabiyansa da dama a wani sumame da suka kai karkarshin rundunar tabbatar da tsaro ta Operation WHIRL.

Rundunar ta bayyana cewa ta yi nasarar kawar da dan bindigan ne yayin da yake tattara mukarrabansa da niyyar kai hari a Karamar Hukumar Igabi da ke Jihar Kaduna.

Kakakin Rundunar, Air Bice Marshal Edward Gabkwet ya shaida wa BBC cewa rundunar ta sami nasarar ne bayan ta dauki lokaci tana dakon gungun ‘yan bindigar kafin su yi dace su yi arangama da su a yankin Gadar Katako da ke Karamar Hukumar Igabi.

‘Lamarin ya auku ne a ranar 18 ga watan Janairu, amma sai bayan ‘yan kwanaki muka sami tabbacin cewa an kashe wannan dan bindiga da mabiyansa. Shi wannan mutumin Janari mun sami labarin cewa yana da hannu cikin harin da aka kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna’, kuma muna da tabbacin cewa yana da hannu a cikin hare-haren da ake kaiwa a hanyar Abuja zuwa Kaduna,’ in ji shi.

Kaduna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
nauru

Maido Da Huldar Diflomasiya Tsakanin Sin Da Nauru Ya Sake Tabbatar Da Matsaya Guda Uku Da Kasashen Duniya Suka Cimma

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.