• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
BUA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Gudanarwar Kamfanin Siminti na BUA, ta sanar da cewa, daga ranar 2 ga watan Oktoba farashin buhun siminti zai koma naira dubu uku da dari biyar (N3,500).

Don haka, yanzu kamfanin zai fara sayar da buhun Siminti kan naira N3,500 sabanin yadda ake sayarwa a baya kan naira dubu N5,000 a wasu wurin ma har zuwa N5,500.

  • Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?
  • Kamfanin BUA Ya Tallafawa Asibitoci 15 A Sakkwato

A cewar kamfanin, wannan wani mataki ne na saukaka wa ‘yan Nijeriya samun damar yin gine-gine da kuma saukaka farashin kayan gini. Inda kamfanin ya ce, akwai wani sabon albishiri da zarar an kammala aikin sabbin layukan da kamfanin ke yi a halin yanzu, zuwa sabuwar shekara, kamfanin zai sake duba yiyuwar rage farashin.

A cewar sanarwar: “Dangane da bayanin da muka fitar a baya na niyyar da muke da shi na rage farashin siminti da zarar mun kammala bude sabbin layukanmu a karshen shekara, domin bunkasa kayan gini da sashin gine-gine.

“A cikin yunkurinmu na rage farashin kayayyakinmu da sake nazartar ayyukanmu lokaci zuwa lokaci, hukumar gudanarwa ta kamfanin BUA tana sanar da abokan cinikayyarta da masu ruwa da tsaki hadi da al’umma cewa daga ranar 2 ga watan Oktoban 2023, mun cimma matsayar rage farashin.

Labarai Masu Nasaba

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

“A kan hakan, daga yanzu za a sayar da buhun simintin BUA ne a kan kudi naira 3,500 domin ‘yan Nijeriya su fara cin gajiyar farashin kafin mu kammala tsare-tsarenmu.”

A cewar sanarwar, wani karin tagomashi ma shi ne, dukkanin wadanda suka yi odar sayo simintin a kan tsohon farashi a halin yanzu, za a duba a maida shi zuwa naira 3,500 a bisa tsarin sabon farashin da zai fara aiki daga ranar 2 ga Oktoba.

Kamfanin ya shawarci dillalanta da su tabbatar jama’a sun amfana da wannan sabon farashin kuma kamfanin zai sanya Ido wajen ganin an bi umarnin amfani da sabon farashin ba tare da tangarda ba.

Idan za a iya tunawa dai Shugaban rukunin kamfanin BUA, Abdul-Samad Rabiu, a kwanain baya lokacin da ya ziyarci shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, ya sanar da cewa, kamfanin ya shirya tsaf domin rage farashin Siminti a Nijeriya zuwa naira N3,500 ko ma kasa da haka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUADangoteSiminti
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

Next Post

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

Related

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
Manyan Labarai

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

7 hours ago
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

10 hours ago
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

12 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

14 hours ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

15 hours ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

15 hours ago
Next Post
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi

August 15, 2025
Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

August 15, 2025
Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.