• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta bayyana cewa tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya shiga hannu, inda ta tsare shi.

Shugaban sashen yada labarai na hukumar EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da kama Yahaya Bello ga manema labarai a ranar Talata.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

Ya ce babban jami’in tsaro na hukumar ne ya kama Yahaya Bello.

A cewarsa, “Gaskiya mun samu nasarar kama shi, yana a hannunmu. Jami’an hukumar ne suka kama shi.”

A baya dai, LEADERSHIP ta ruwaito rahoto cewa Yahaya Bello ya je hedikwatar EFCC ne a safiyar ranar Talata tare da lauyoyinsa domin amsa tuhumar da ake masa na karkatar da kudade ba bisa ka’ida ba, wanda a bayan watanni ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

An bayyana cewa tsohon gwamnan ya je ofishin EFCC ne da lauyoyinsa ba tare da magajinsa ba, Gwamna Usman Ododo na Jihar Kogi, wanda ya biyo shi ofishin EFCC makonnin da suka gabata.

LEADERSHIP ta samu labarin cewa wata tawagar masu bincike sun tsare Yahaya Bello a hedikwatar hukumar EFCC da ke gundumar Jabi a Abuja.

Idan dai za a iya tunawa a ranar 18 ga watan Afrilun 2024 ne hukumar ta ayyana tsohon gwamnan a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo tare da bayyana takardar sammacin kama shi kan zargin da ake masa na karkatar da kudade na naira biliyan 80.2.

A zaman karshe na shari’ar da aka yi masa a kotu na ranar 14 ga watan Nuwamba, EFCC ta bukaci a dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Nuwamba a sabuwar shari’ar da ta shigar a kan Yahaya Bello, inda ta ce har yanzu kwanaki 30 za ta ci gaba da neman sammacin da aka yi a baya.

Sai dai hukumar EFCC ta amince da bayar da belin wadanda ake tuhumar Yahaya Bello da Umar Oricha, da Abdulsalami Hudu, inda ta kuma bukaci kotu ta kara wa wanda ake tuhuma na farko wato Yahaya Bello wa’adi domin gurfana a gaban kotu. Mai yiwuwa a gurfanar da tsohon gwamnan a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCC
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Taron Ƙungiyar Baburawa Na Abuja Cikin Annashuwa

Next Post

Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

8 hours ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

10 hours ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

May 31, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.