• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
EFCC

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta bayyana cewa tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya shiga hannu, inda ta tsare shi.

Shugaban sashen yada labarai na hukumar EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da kama Yahaya Bello ga manema labarai a ranar Talata.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

Ya ce babban jami’in tsaro na hukumar ne ya kama Yahaya Bello.

A cewarsa, “Gaskiya mun samu nasarar kama shi, yana a hannunmu. Jami’an hukumar ne suka kama shi.”

A baya dai, LEADERSHIP ta ruwaito rahoto cewa Yahaya Bello ya je hedikwatar EFCC ne a safiyar ranar Talata tare da lauyoyinsa domin amsa tuhumar da ake masa na karkatar da kudade ba bisa ka’ida ba, wanda a bayan watanni ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

An bayyana cewa tsohon gwamnan ya je ofishin EFCC ne da lauyoyinsa ba tare da magajinsa ba, Gwamna Usman Ododo na Jihar Kogi, wanda ya biyo shi ofishin EFCC makonnin da suka gabata.

LEADERSHIP ta samu labarin cewa wata tawagar masu bincike sun tsare Yahaya Bello a hedikwatar hukumar EFCC da ke gundumar Jabi a Abuja.

Idan dai za a iya tunawa a ranar 18 ga watan Afrilun 2024 ne hukumar ta ayyana tsohon gwamnan a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo tare da bayyana takardar sammacin kama shi kan zargin da ake masa na karkatar da kudade na naira biliyan 80.2.

A zaman karshe na shari’ar da aka yi masa a kotu na ranar 14 ga watan Nuwamba, EFCC ta bukaci a dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Nuwamba a sabuwar shari’ar da ta shigar a kan Yahaya Bello, inda ta ce har yanzu kwanaki 30 za ta ci gaba da neman sammacin da aka yi a baya.

Sai dai hukumar EFCC ta amince da bayar da belin wadanda ake tuhumar Yahaya Bello da Umar Oricha, da Abdulsalami Hudu, inda ta kuma bukaci kotu ta kara wa wanda ake tuhuma na farko wato Yahaya Bello wa’adi domin gurfana a gaban kotu. Mai yiwuwa a gurfanar da tsohon gwamnan a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.