• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta bayyana cewa tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya shiga hannu, inda ta tsare shi.

Shugaban sashen yada labarai na hukumar EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da kama Yahaya Bello ga manema labarai a ranar Talata.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

Ya ce babban jami’in tsaro na hukumar ne ya kama Yahaya Bello.

A cewarsa, “Gaskiya mun samu nasarar kama shi, yana a hannunmu. Jami’an hukumar ne suka kama shi.”

A baya dai, LEADERSHIP ta ruwaito rahoto cewa Yahaya Bello ya je hedikwatar EFCC ne a safiyar ranar Talata tare da lauyoyinsa domin amsa tuhumar da ake masa na karkatar da kudade ba bisa ka’ida ba, wanda a bayan watanni ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

An bayyana cewa tsohon gwamnan ya je ofishin EFCC ne da lauyoyinsa ba tare da magajinsa ba, Gwamna Usman Ododo na Jihar Kogi, wanda ya biyo shi ofishin EFCC makonnin da suka gabata.

LEADERSHIP ta samu labarin cewa wata tawagar masu bincike sun tsare Yahaya Bello a hedikwatar hukumar EFCC da ke gundumar Jabi a Abuja.

Idan dai za a iya tunawa a ranar 18 ga watan Afrilun 2024 ne hukumar ta ayyana tsohon gwamnan a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo tare da bayyana takardar sammacin kama shi kan zargin da ake masa na karkatar da kudade na naira biliyan 80.2.

A zaman karshe na shari’ar da aka yi masa a kotu na ranar 14 ga watan Nuwamba, EFCC ta bukaci a dage sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Nuwamba a sabuwar shari’ar da ta shigar a kan Yahaya Bello, inda ta ce har yanzu kwanaki 30 za ta ci gaba da neman sammacin da aka yi a baya.

Sai dai hukumar EFCC ta amince da bayar da belin wadanda ake tuhumar Yahaya Bello da Umar Oricha, da Abdulsalami Hudu, inda ta kuma bukaci kotu ta kara wa wanda ake tuhuma na farko wato Yahaya Bello wa’adi domin gurfana a gaban kotu. Mai yiwuwa a gurfanar da tsohon gwamnan a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCC
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Taron Ƙungiyar Baburawa Na Abuja Cikin Annashuwa

Next Post

Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

3 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

3 weeks ago
Next Post
Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

Harry Maguire Ya Sanya Hannun Kwantaragin Shekara Ɗaya A Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.