• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakarun Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Dakarun Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla ‘yan ta’addar ISWAP 19 ne suka rasa rayukansu a lokacin da dakarun Operation HADIN KAI suka fatattakie su a Gamboru Ngala da ke karamar hukumar Ngala a Jihar Borno. 

Gamboru, wani gari ne mai iyaka da ke nisan kusan kilomita 128 zuwa Maiduguri, babban birnin jihar.

  • Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku
  • Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

LEADERSHIP ta tattaro cewa sojojin tare da wata rundunar hadin gwiwa ta Civilian Joint Task Force (CJTF) sun cimma wannan nasara ne a ranar Talata, 11 ga watan Oktoba, 2022 bayan da suka dakile wani harin kwantan bauna da ‘yan ta’addan suka kai wa sojojin.

Wani rahoton leken asirin da Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin Chadi ya samu daga manyan majiyoyin soji, wanda wakilinmu ya nakalto, ya bayyana cewa ‘yan ta’addan da suka zo da adadi mai yawa a kan babura da mota kirar Hilux dauke da bindigu, sun fara kai harin kan sojojin.

Majiyoyin leken asirin sun ce dakarun da ke da karfin gwiwa sun yi musu kwantan bauna wanda ya haifar da kazamin fadan da ya dauki tsawon mintuna 40 ana yi.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Ya ce daga baya sojojin sun mamaye ‘yan ta’addan da karfin wuta wanda hakan ya sa suka tsere.

“Sojojin dai sun fatattaki ‘yan ta’addan da suka koma baya tare da kashe 19 daga cikinsu.

“Sojojin sun yi nasarar kama wata mota dauke da bindigu tasu bayan sun kashe dukkan mutanen da ke cikinta, sun kwato babura tara da kuma makamai da dama da suka hada da PKT daya, AK-47 guda tara da harsashi da dama.

“Ba a samu asarar rai ba a bangaren sojojin saboda biyu ne kawai suka samu rauni a bangarenmu,” in ji wata majiya.

LEADERSHIP ta rawaito cewa sojoji da rundunar hadin gwiwa sun samu nasarar ne biyo bayan bayanan sirri da suka samu a garin Gamborun Ngala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBornoDakarun SojiGomboru NgalaISWAP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku

Next Post

Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

2 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

3 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

11 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

15 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

16 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

18 hours ago
Next Post
Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.