ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakarun Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 

by Sadiq
4 years ago
ISWAP

Akalla ‘yan ta’addar ISWAP 19 ne suka rasa rayukansu a lokacin da dakarun Operation HADIN KAI suka fatattakie su a Gamboru Ngala da ke karamar hukumar Ngala a Jihar Borno. 

Gamboru, wani gari ne mai iyaka da ke nisan kusan kilomita 128 zuwa Maiduguri, babban birnin jihar.

  • Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku
  • Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

LEADERSHIP ta tattaro cewa sojojin tare da wata rundunar hadin gwiwa ta Civilian Joint Task Force (CJTF) sun cimma wannan nasara ne a ranar Talata, 11 ga watan Oktoba, 2022 bayan da suka dakile wani harin kwantan bauna da ‘yan ta’addan suka kai wa sojojin.

ADVERTISEMENT

Wani rahoton leken asirin da Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin Chadi ya samu daga manyan majiyoyin soji, wanda wakilinmu ya nakalto, ya bayyana cewa ‘yan ta’addan da suka zo da adadi mai yawa a kan babura da mota kirar Hilux dauke da bindigu, sun fara kai harin kan sojojin.

Majiyoyin leken asirin sun ce dakarun da ke da karfin gwiwa sun yi musu kwantan bauna wanda ya haifar da kazamin fadan da ya dauki tsawon mintuna 40 ana yi.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya ce daga baya sojojin sun mamaye ‘yan ta’addan da karfin wuta wanda hakan ya sa suka tsere.

“Sojojin dai sun fatattaki ‘yan ta’addan da suka koma baya tare da kashe 19 daga cikinsu.

“Sojojin sun yi nasarar kama wata mota dauke da bindigu tasu bayan sun kashe dukkan mutanen da ke cikinta, sun kwato babura tara da kuma makamai da dama da suka hada da PKT daya, AK-47 guda tara da harsashi da dama.

“Ba a samu asarar rai ba a bangaren sojojin saboda biyu ne kawai suka samu rauni a bangarenmu,” in ji wata majiya.

LEADERSHIP ta rawaito cewa sojoji da rundunar hadin gwiwa sun samu nasarar ne biyo bayan bayanan sirri da suka samu a garin Gamborun Ngala.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.