• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakarun Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 19 A Wata Arangama A Borno 

bySadiq
3 years ago
ISWAP

Akalla ‘yan ta’addar ISWAP 19 ne suka rasa rayukansu a lokacin da dakarun Operation HADIN KAI suka fatattakie su a Gamboru Ngala da ke karamar hukumar Ngala a Jihar Borno. 

Gamboru, wani gari ne mai iyaka da ke nisan kusan kilomita 128 zuwa Maiduguri, babban birnin jihar.

  • Idan Aka Zabi PDP, Za Mu Kawo Karshen Matsalar Tsaro – Atiku
  • Ya Shiga Hannu Kan Siyar Wa Mutane Garin Katako Da Siminti A Matsayin Maganin Gargajiya A Kwara

LEADERSHIP ta tattaro cewa sojojin tare da wata rundunar hadin gwiwa ta Civilian Joint Task Force (CJTF) sun cimma wannan nasara ne a ranar Talata, 11 ga watan Oktoba, 2022 bayan da suka dakile wani harin kwantan bauna da ‘yan ta’addan suka kai wa sojojin.

Wani rahoton leken asirin da Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci a yankin tafkin Chadi ya samu daga manyan majiyoyin soji, wanda wakilinmu ya nakalto, ya bayyana cewa ‘yan ta’addan da suka zo da adadi mai yawa a kan babura da mota kirar Hilux dauke da bindigu, sun fara kai harin kan sojojin.

Majiyoyin leken asirin sun ce dakarun da ke da karfin gwiwa sun yi musu kwantan bauna wanda ya haifar da kazamin fadan da ya dauki tsawon mintuna 40 ana yi.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Ya ce daga baya sojojin sun mamaye ‘yan ta’addan da karfin wuta wanda hakan ya sa suka tsere.

“Sojojin dai sun fatattaki ‘yan ta’addan da suka koma baya tare da kashe 19 daga cikinsu.

“Sojojin sun yi nasarar kama wata mota dauke da bindigu tasu bayan sun kashe dukkan mutanen da ke cikinta, sun kwato babura tara da kuma makamai da dama da suka hada da PKT daya, AK-47 guda tara da harsashi da dama.

“Ba a samu asarar rai ba a bangaren sojojin saboda biyu ne kawai suka samu rauni a bangarenmu,” in ji wata majiya.

LEADERSHIP ta rawaito cewa sojoji da rundunar hadin gwiwa sun samu nasarar ne biyo bayan bayanan sirri da suka samu a garin Gamborun Ngala.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

Yin Kasuwanci Tare Da Kasar Sin Shi Ne Zabin Karin Kamfanonin Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version