• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

by Abubakar Abba
2 years ago
Manja

Kwararru a fannin noman Kwakwar Manja sun yi kira da a zuba jari a nomanta, mussaman don a kara bunkasa nomanta a kasar nan.

A wata hira da ban da ban da aka yi da su a jihar Legas, kwararrun sun mayar da martani ne kan rahoton da aka wallafa a kwanan baya cewa, Nijeriya ta shigo da Manja da kudinsa ya kai Naira biliyan 299.6 daga 2017 zuwa 2022.

  • Sudan: Jami’o’in Nijeriya Sun Sha Alwashin Bai Wa Daliban Da Aka Kwaso Guraben Karatu
  • Burin Bai Wa Jama’a Shawarwari Ya Sa Na Fara Waka – Jamilu JEY BOY

Rahoton na tsakiyar shekara wanda hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta wallafa ya nuna cewa, Danyen Manjan na daga cikin manyan kaya biyar da ake shigo wa da su cikin Nijeriya.

Daya daga cikin kwararru Farfesa  Adetunji Iyiola ya koka kan yadda ake shigo da Manjan cikin kasar nan,duk da cewa Nijeriya ta kasance kasar noma.

A cewar Iyiola, akwai bukatar a habaka noman Kwakwar Manja a kasar nan, musamman ta hanyar yin amfani da dabarun zamani ma yin noma.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Ya bayyana cewa,ganin cewa fannin ana samun dimbin kudaden shiga, akwai bukatar a zuba jari mai yawa a fannin a kasar nan tare da kuma zuba jari wajen sarrafa shi.

“Muna da mutane masu kunbar susu da dama a kasar nan a saboda haka akwai bukatar su zuba jarinsu a fannin wajen nomanta da kuma sarrafa ta yadda za ta kai har ana fitar da ita zuwa ketare.

A cewarsa, a zaman mu na kasar, bai kamata ace muna shigo da Manja ba domin Allah ya wadace mu da kasar yin noma mai kyau, musamman a jihohin Osun da Ondo.

Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta zuba jari a fannin, mussaman wajen kara fadada noma noman ma Kwakwar Manja a kasar nan , inda ya kara da cewa, akwai kuma bukatar a samar wa da manoman na Kwakwar Manja kayan nomanta na zamani don a kara samar da ita fa yawa a kasar nan.

A cewarsa, akwai kuma bukatar gwamnatin ta kara taimaka wa masu sarrafa ta a cikin kasar, inda hakan zai sa a rage shigo da ita daga kasar waje, mussaman don a kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Shi ma a na sa bangaren daya kwararen a fannin Mista Akin Alabi yk bayyana cewa, dole ne a kara yin kokari wajen sarrafa ta a cikin kasar nan, mussaman don a rage shigo da ita daga kasar waje.

Ya bayyana cewa, akwai kuma bukatar a samar wa da manoman ta ingantacce Iri don su samu riba mai yawa bayan sun yi girbi.

Ya sanar da cewa, muna da bukatar samun masu noman Kwakwar Manja a kasar nan domin muna da kasar yin noma mai kyau.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

June 21, 2025
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

January 11, 2025
Next Post
Tsokaci Kan Maza Masu Boye Bayanan Kansu Wurin Neman Aure

Tsokaci Kan Maza Masu Boye Bayanan Kansu Wurin Neman Aure

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

EFCC Ta Ƙwato Kadarorin Naira Biliyan 500 A Ƙarƙashin Gwamnatin Tinubu – Shettima

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.