• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibai Sun Yi Kira Da A Kara Hanyoyin Ba Matasa Bashin Karatu

by Idris Aliyu Daudawa
11 months ago
in Ilimi
0
Dalibai Sun Yi Kira Da A Kara Hanyoyin Ba Matasa Bashin Karatu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar daliban kwalejojin ilimi ta kasa ta yi kira da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da sauran ‘yan Nijeriya masu sha’awar bunkasa lamarin ilimi su kara taimakawa da kudi a matsayin bashi ko kuma taimako, domin taimakawa matasan Nijeriya da dalibai wadanda a halin da ake ciki basu da aikin yi, da idan ba sa a aka yi ba suna iya shiga wani hali na aikata ashsha,saboda halin da ake ciki na tsadar kayar abinci a sanadiyar karin kudin manfetur.

Sanarwar da Shugabanta  Egunjobi Samuel Oluwaseun,ya raba wa manewa labarai ranar Litinin ta makon da muke ciki a Abuja, ya ce akwai dalibai milyan 12.5,a kwalejojin ilimi  million  219 da ake da su a duk fadin Nijeriya,ya jinjina wa kokarin da Shugaban kasa yake yi kan rage fatara, inda kuma suka yi kira da shi cewar ya ci gaba da aiki mai kyau da yake yi.

  • Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa
  • An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar ‘Yan Shi’a A Yobe

Ya ce, “Idan aka kara kudaden yin hakan zai zai kara taimakawa a kan irin tubalin yin ginin hakan da aka fara wadanda gwamnatocin baya suka yi, wanda kuma hukumar NIRSAL ce jagorar yin hakan ta hanyar Microfinance Bank (NMFB), wanda ya samar da ayyukan yi a kai tsaye ko kuma akasin haka, lamarin da yayi sanadiyar raba wasu da fatara.”

Kunguyar ta dalibai ta jinjinawa jagorancin Abdullahi Abubakar Kure a matsayin Shugaban na Bankin Microfinance karkashin NIRSAL,kan irin namijin aikin da yake yi.

Ya kara jaddada cewa NMFB ita kadai ce hukuma wadda ta raba kudaden kawo dauki a cikin gaskiya da rikon amana,a sassa shida na kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

“Mutane sun samu dama ta samun bashin ba tare da taimakon wani daga cikin ofishin ba, maganar gaskiya kuma ire-iren wadancan kudaden ta ba wasu damar ga matasa bunkasa sana’arsu, wasu kuma sun fara, da kuma cigaba da harkar har zuwa halin da ake ciki yanzu” kamar yadda yace.

“Duk da yake dai wadanda suka amfana da kudaden sun so ace anbasu kudaden a matsayin tallafi ne amma Bankin ya cigaba da fada masu ai bashi ne aka basu.Duk dai yadda abin ya kasance kudaden sun  taimaka wajen bunkasa kananan sana’oi a Nijeriya.

Daga karshe ya ce “Idan aka tuna da tsarin mulkin gwamnatin Shugaban kasa Bola Bola Ahmed Tinubu, abu maikyau ne da kuma fa’ida ga ita gwamnatin ta shi ta kara bada kudade a bangarori na kanana da matsakaitan sana’oi da kuma aikin gona, domin hakan zai taimakawa ‘yan Nijeriya su samu hanyar da za su dogara da ita saboda su samu kyakkyawar rayuwa,”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimJami'aSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Ta Zanta Da Uwargidan Shugaban Kongon Brazzaville

Next Post

Shugaban Namibia: Batun Bunkasuwa Yana Da Nasaba Da Kasar Sin

Related

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

6 days ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

2 weeks ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

2 weeks ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

2 weeks ago
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya
Ilimi

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

2 weeks ago
Next Post
Shugaban Namibia: Batun Bunkasuwa Yana Da Nasaba Da Kasar Sin

Shugaban Namibia: Batun Bunkasuwa Yana Da Nasaba Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.