• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci Duk Da Karuwar Kudin Shiga – Masana

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Dalilan Da Suka Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci Duk Da Karuwar Kudin Shiga – Masana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana tattalin arziki da kwararru a bangaren hada-hadar kudi a Nijeriya sun yi bayanin dalilan da suke janyo har yanzu al’ummar Nijeriya ke fama da talauci da fatara duk kuwa da cewa a ‘yan watannin da suka gabata tattalin arzikin kasar (GDP) ya karu da kaso 3.46 a zango na uku na shekarar 2024.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da daraktan kididdiga na tarayya, Adeyemi Adeniran Adedeji, ya sanar a ranar Litinin cewa tattalin arzikin Nijeriya ya fadada zuwa da kaso 3.49 a zango na uku na 2024 daga kaso 3.19 a zango na biyu na 2024.

  • IPAC: Tasiri Ko Rashin Tasirinta A Siyasar Nijeriya
  • Nijeriya Na Buƙatar Naira Tiriliyan 1 Don Kawo Ƙarshen Cin Zarafin Mata –Bankin Duniya

Bangarorin da suka taimaka wajen karuwar tattalin arzikin Nijeriya sun hada da sashin ayyuka, cibiyoyin hada-hadar kudade, kamfanonin sadarwa, noma, sufuri da kuma bangaren gine-gine.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta wata sanarwar da kakakinsa Sunday Dare, ya nuna gayar farin cikinsa kan ci gaban da tattalin arzikin cikin gida ya samu. Inda ya misalta hakan da cewa zai kara kyautata tattalin arziki.

Sai dai kuma duk da karuwar lambobin a bangarorin, wannan lamarin bai nuna wani tasiri ga rayuwar al’ummar Nijeriya ba. A zahirance dai, ‘yan Nijeriya na fuskantar hauhawar farashin kayayyakin masarufi, wanda ya kasance kaso 33.87 da kaso 39.16 a watan Oktoba. Hauhawar farashin na ta da wa al’umman kasa hankali da jefa su cikin matsin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Da yake maida martani kan wannan matakin a hirarsa da ‘yan jarida, tsohon shugaban majalisar cibiyar kwararrun ma’aikatan banki (CIB), Farfesa Segun Ajibola, ya ce, akwai bambanci tsakanin ma’aunin tattalin arziki da kuma halin zahiri da al’umma ke ciki.

Ya ce karuwar GDP bai wadatar ba wajen samar da yanayin kyautata tattalin arzikin jama’a. A cewarsa, rashin kyan tsare-tsaren da suke akwai su ne suka sabbaba ake samun nakasu daga sauya tattalin arziki zuwa saukaka rayuwa ga jama’a.

“Akwai bambanci sosai wajen shigar da tattalin arzikin Nijeriya zuwa amfanun rayuwar al’umma. Inganta ma’aunin tattalin arziki dole ne, amma babu isassun yanayin inganta walwalar tattalin arzikin jama’a.

“Alkaluma irinsu bunkasar tattalin arziki, ajiyar kudaden waje, rabon bashi, da dai sauransu, sun kafa hanya da samar da ingantacciyar rayuwa ga mafiya yawan marasa karfi a kasa kamar Nijeriya.

“Nijeriya na ci gaba da shaida ci gaba duk da cewa ana samun canjin daga shekarun 1970, amma yawancin jama’a su na fama da talauci saboda rashin daidaito da rashin kyawawan tsari.”

Shi ma babban daraktan cibiyar habaka harkokin kasuwanci masu zaman kansu (PPE), Muda Yusuf, ya ce karuwa GDP ci gaba ne mai ma’ana ga kasar, sai dai ya nemi gwamnati da ta bijiro da tsare-tsaren da suka dace da za su inganta walwalar jama’a.

Kazalika, babban jami’in ‘SD & D Capital Management,’ Mista Idakolo Gbolade, ya ce kididdigar sam ba ta yi daidai da yanayin hauhawar farashin kaya da ake fuskanta ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tawagar Mu’amalar Al’adu Ta Xinjiang Ta Kasar Sin Ta Kai Ziyara Turkiye Da Saudiyya Da Qatar

Next Post

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Related

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna
Labarai

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

4 hours ago
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Manyan Labarai

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

8 hours ago
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?
Labarai

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

10 hours ago
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa
Labarai

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

11 hours ago
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
Labarai

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

12 hours ago
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

12 hours ago
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

LABARAI MASU NASABA

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.