ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci Duk Da Karuwar Kudin Shiga – Masana

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Nijeriya

Masana tattalin arziki da kwararru a bangaren hada-hadar kudi a Nijeriya sun yi bayanin dalilan da suke janyo har yanzu al’ummar Nijeriya ke fama da talauci da fatara duk kuwa da cewa a ‘yan watannin da suka gabata tattalin arzikin kasar (GDP) ya karu da kaso 3.46 a zango na uku na shekarar 2024.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da daraktan kididdiga na tarayya, Adeyemi Adeniran Adedeji, ya sanar a ranar Litinin cewa tattalin arzikin Nijeriya ya fadada zuwa da kaso 3.49 a zango na uku na 2024 daga kaso 3.19 a zango na biyu na 2024.

  • IPAC: Tasiri Ko Rashin Tasirinta A Siyasar Nijeriya
  • Nijeriya Na Buƙatar Naira Tiriliyan 1 Don Kawo Ƙarshen Cin Zarafin Mata –Bankin Duniya

Bangarorin da suka taimaka wajen karuwar tattalin arzikin Nijeriya sun hada da sashin ayyuka, cibiyoyin hada-hadar kudade, kamfanonin sadarwa, noma, sufuri da kuma bangaren gine-gine.

ADVERTISEMENT

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta wata sanarwar da kakakinsa Sunday Dare, ya nuna gayar farin cikinsa kan ci gaban da tattalin arzikin cikin gida ya samu. Inda ya misalta hakan da cewa zai kara kyautata tattalin arziki.

Sai dai kuma duk da karuwar lambobin a bangarorin, wannan lamarin bai nuna wani tasiri ga rayuwar al’ummar Nijeriya ba. A zahirance dai, ‘yan Nijeriya na fuskantar hauhawar farashin kayayyakin masarufi, wanda ya kasance kaso 33.87 da kaso 39.16 a watan Oktoba. Hauhawar farashin na ta da wa al’umman kasa hankali da jefa su cikin matsin rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Da yake maida martani kan wannan matakin a hirarsa da ‘yan jarida, tsohon shugaban majalisar cibiyar kwararrun ma’aikatan banki (CIB), Farfesa Segun Ajibola, ya ce, akwai bambanci tsakanin ma’aunin tattalin arziki da kuma halin zahiri da al’umma ke ciki.

Ya ce karuwar GDP bai wadatar ba wajen samar da yanayin kyautata tattalin arzikin jama’a. A cewarsa, rashin kyan tsare-tsaren da suke akwai su ne suka sabbaba ake samun nakasu daga sauya tattalin arziki zuwa saukaka rayuwa ga jama’a.

“Akwai bambanci sosai wajen shigar da tattalin arzikin Nijeriya zuwa amfanun rayuwar al’umma. Inganta ma’aunin tattalin arziki dole ne, amma babu isassun yanayin inganta walwalar tattalin arzikin jama’a.

“Alkaluma irinsu bunkasar tattalin arziki, ajiyar kudaden waje, rabon bashi, da dai sauransu, sun kafa hanya da samar da ingantacciyar rayuwa ga mafiya yawan marasa karfi a kasa kamar Nijeriya.

“Nijeriya na ci gaba da shaida ci gaba duk da cewa ana samun canjin daga shekarun 1970, amma yawancin jama’a su na fama da talauci saboda rashin daidaito da rashin kyawawan tsari.”

Shi ma babban daraktan cibiyar habaka harkokin kasuwanci masu zaman kansu (PPE), Muda Yusuf, ya ce karuwa GDP ci gaba ne mai ma’ana ga kasar, sai dai ya nemi gwamnati da ta bijiro da tsare-tsaren da suka dace da za su inganta walwalar jama’a.

Kazalika, babban jami’in ‘SD & D Capital Management,’ Mista Idakolo Gbolade, ya ce kididdigar sam ba ta yi daidai da yanayin hauhawar farashin kaya da ake fuskanta ba.

Nijeriya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.