ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci Duk Da Karuwar Kudin Shiga – Masana

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Nijeriya

Masana tattalin arziki da kwararru a bangaren hada-hadar kudi a Nijeriya sun yi bayanin dalilan da suke janyo har yanzu al’ummar Nijeriya ke fama da talauci da fatara duk kuwa da cewa a ‘yan watannin da suka gabata tattalin arzikin kasar (GDP) ya karu da kaso 3.46 a zango na uku na shekarar 2024.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da daraktan kididdiga na tarayya, Adeyemi Adeniran Adedeji, ya sanar a ranar Litinin cewa tattalin arzikin Nijeriya ya fadada zuwa da kaso 3.49 a zango na uku na 2024 daga kaso 3.19 a zango na biyu na 2024.

  • IPAC: Tasiri Ko Rashin Tasirinta A Siyasar Nijeriya
  • Nijeriya Na Buƙatar Naira Tiriliyan 1 Don Kawo Ƙarshen Cin Zarafin Mata –Bankin Duniya

Bangarorin da suka taimaka wajen karuwar tattalin arzikin Nijeriya sun hada da sashin ayyuka, cibiyoyin hada-hadar kudade, kamfanonin sadarwa, noma, sufuri da kuma bangaren gine-gine.

ADVERTISEMENT

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta wata sanarwar da kakakinsa Sunday Dare, ya nuna gayar farin cikinsa kan ci gaban da tattalin arzikin cikin gida ya samu. Inda ya misalta hakan da cewa zai kara kyautata tattalin arziki.

Sai dai kuma duk da karuwar lambobin a bangarorin, wannan lamarin bai nuna wani tasiri ga rayuwar al’ummar Nijeriya ba. A zahirance dai, ‘yan Nijeriya na fuskantar hauhawar farashin kayayyakin masarufi, wanda ya kasance kaso 33.87 da kaso 39.16 a watan Oktoba. Hauhawar farashin na ta da wa al’umman kasa hankali da jefa su cikin matsin rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Da yake maida martani kan wannan matakin a hirarsa da ‘yan jarida, tsohon shugaban majalisar cibiyar kwararrun ma’aikatan banki (CIB), Farfesa Segun Ajibola, ya ce, akwai bambanci tsakanin ma’aunin tattalin arziki da kuma halin zahiri da al’umma ke ciki.

Ya ce karuwar GDP bai wadatar ba wajen samar da yanayin kyautata tattalin arzikin jama’a. A cewarsa, rashin kyan tsare-tsaren da suke akwai su ne suka sabbaba ake samun nakasu daga sauya tattalin arziki zuwa saukaka rayuwa ga jama’a.

“Akwai bambanci sosai wajen shigar da tattalin arzikin Nijeriya zuwa amfanun rayuwar al’umma. Inganta ma’aunin tattalin arziki dole ne, amma babu isassun yanayin inganta walwalar tattalin arzikin jama’a.

“Alkaluma irinsu bunkasar tattalin arziki, ajiyar kudaden waje, rabon bashi, da dai sauransu, sun kafa hanya da samar da ingantacciyar rayuwa ga mafiya yawan marasa karfi a kasa kamar Nijeriya.

“Nijeriya na ci gaba da shaida ci gaba duk da cewa ana samun canjin daga shekarun 1970, amma yawancin jama’a su na fama da talauci saboda rashin daidaito da rashin kyawawan tsari.”

Shi ma babban daraktan cibiyar habaka harkokin kasuwanci masu zaman kansu (PPE), Muda Yusuf, ya ce karuwa GDP ci gaba ne mai ma’ana ga kasar, sai dai ya nemi gwamnati da ta bijiro da tsare-tsaren da suka dace da za su inganta walwalar jama’a.

Kazalika, babban jami’in ‘SD & D Capital Management,’ Mista Idakolo Gbolade, ya ce kididdigar sam ba ta yi daidai da yanayin hauhawar farashin kaya da ake fuskanta ba.

Nijeriya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.