• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IPAC: Tasiri Ko Rashin Tasirinta A Siyasar Nijeriya

by Alhaji Adamu Rabiu and Abubakar Sulaiman
7 months ago
in Bakon Marubuci
0
IPAC: Tasiri Ko Rashin Tasirinta A Siyasar Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sahihancin Kungiyar Gamayyar Jam’iyyun Siyasar Nijeriya:

Mafi akasarin ‘yan Nijeriya, sun dawo daga rakiyar siyasa; domin kuwa fagen a halin yanzu ya zama na wadanda suka kware a fagen cin amana da rashin gaskiya da yaudara da cuta da kuma makirci. Haka nan, su ma jam’iyyun siyasa suna fifita son kai fiye da son Nijeriyar da kuma halin da ‘yan kasa ke ciki. Yayin da su kuma mabiya da sauran ’yan kasa suka samu kansu a cikin wani irin yanayi, sakamakon yin watsi da aka yi da al’amuransu ta hanyar ko-in-kula da halin da suke ciki.

 

A cikin wannan yanayi na rudanin siyasa, Nijeriya ta tsinci kanta a cikin yanayin da ya yi kama da teku; inda igiyar ruwa ke girgiza ta tare da jan ta, da alama kuma tana kara nitsewa cikin tekun baharmaliyar demokaradiyya.

 

Labarai Masu Nasaba

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

Saboda haka, a wannan hali da ake ciki; ‘yan Nijeriya na matukar bukatar jirgin ruwan da za su shiga ya kai su tudun mun tsira, kwatsam a cikin wannan yanayi na  hadari sai ga  jirgin ruwan ‘Inter-Party Adbisory Council’ IPAC, (Gamayyar Jam’iyyun Siyasun Nijeriya).

 

Abin tambaya a nan shi ne, shin anya wannan jirgin zai iya kai ‘yan Nijeriya tudun mun tsira ko kuwa bai zai iya tseratar da su daga ruwan da ya yi kama da ruwan dufanan wannan demokaradiyya?  Wannan na nuni da cewa, IPAC da alama ta samu kanta cikin wani mawuyacin hali yanzu.

 

Har ila yau, makasudin kafa IPAC shi ne, don samar da kyakkyawan yanayin hadin kai tsakani jam’iyyun siyasa a Nijeriya, inda kuma za ta samar da daidaito tare da bayar da dama ta hanyar da jam’iyyun siyasar za su samu filin bayar da tasu gudunmawar wajen ci gaban Nijeriya. A hannu guda kuma, ta samar da mafita ga ‘yan Nijeriya, sakamakon yadda aka dade ana gasa musu aya a hannu.

 

Amma kash! A aikace IPAC ta kasa cimma wannan buri wajen ciyar da siyasar Nijeriyar gaba, inda ta zama abin tausayi tare da zama kamar ‘yar Mowa.

 

Tambaya Mai Muhimmanci Mai Kuma Bukatar Amsa:

Shin IPAC za ta iya ciyar da demokaradiyyar Nijeriya gaba tare da samar mata da mafita ko kuwa ta zamo wani abu ne daban; wanda manyan jam’ iyyu ke amfani da ita wajen cimma burikansu a siyasance?

 

Darajar IPAC: Shin Fitila Ce Mai Haske A Cikin Hazo?

Shin mai ya faru da IPAC? Amsar tana cikin gazawar sanin muhimmancin hadin kai da kuma tafiyar bai- daya a aikace. IPAC ya kamata ta zama mai kara kuzari wajen gwagwarmayar samun canji, ba kawai dakin babban taron tattaunawa ba, sannan kuma ya kamata ta zama wata inuwa wadda ‘yan Nijeriyan da ba su da uwa a bakin murhu; za su iya zuwa su samu mafita. A cikin wannan rudani IPAC ta rasa wata turba mai daraja a wajen ‘yan Nijeriya.

 

Duk da halin da a ke ciki yanzu, ka da mu  yanke kauna daga samun sa’ida, domin kuwa akwai wata  dama da za a iya samun canji, amma idan an samu canjin fahimta a cikin kungiyar IPAC din, an kuma samu yardar cewa Nijeriya ita ce gaba, ba san rai ko fifita wata jam’iyya ba. Wannan kuwa zai samu ne kadai idan:

  1. Akwai Hadin Kai: IPAC a matsayin lema ga dukkanin jam’iyyun siyasu a Nijeriya, ya kamata ta zama wani wurin na hadin gwiwa, wanda duk jam’íyyu za su zama tsaran juna ba abokan gaba ba.
  2. An Samu Canji Mai Ma’ana:

IPAC ya kamata ta zama wani dandamali; wanda jam’iyyun siyasa za su samu damar bayar da tasu gudunmawar wajen ci gaban siyasa a Nijeriya .

  1. Akwai Hadin Gwiwa Da Taimakekeniya:

Haka nan, ya kamata IPAC ta zama ‘tsintsiya madauri daya’ , idan jam’iyyu za su samu fagen taimakekeniya a tsakaninsu tare da yin tasiri a fagen siyasar Nijeriya, ko shakka babu, za ta zama kamar wani hasken wuta mai  yi wa jiragen ruwa jagora zuwa bakin teku.

  1. Ginshikin Adalci:

Ya kamata IPAC ta zama wani waje ne, wanda ‘yan siyasa za su samu horo; ta yadda adalci da rikon amana zai rika wanzuwa.

 

Tsara Sabon Tattakin Siyasa A Nijeriya

Babu shakka, lokaci ya yi da ‘yan siyasar Nijeriya za su yi  karatun ta-nutsu, su kuma rungumi harkar siyasa da hannu biyu, inda gaskiya da rikon amana da sadaukar da kai zai kasance a matsayin gaba; ba yin magudi ko ha’inci ba.

 

Har ila yau, wajibi ne mu kwana da sanin cewa, hakkin duk dan Nijeriya ne bayar da tasa gudunmawar wajen ci gaban kasa da kuma ‘yan kasa. Haka nan kuma, yanzu ya zama wajibi masu madafun iko da zababbun ‘yan majalisa, su kasance masu bayar da bayanai tare da ba’asi bisa alkawarurrukan zabe da suka yi da kuma daukar alhaki na kin cika wanna alkawarurruka da suka yi.

 

Haka zalika, wannan tafiya ta kowane dan Nijeriya ce, wanda ke fatan ganin wayewar gari mai cike da walwala da jindadi.

 

A karshe, ci gaban demokaradiyya ba hawan manyan motoci ba ne, ko gina manyan gidaje ko wawure dokiyar kasa ba, ci gaban siyasa shi ne samun ingantaciyar rayuwar ‘yan kasa cikin aminci da daraja. Yanzu lokaci ya yi da Nijeriya za ta samu shugabanni jajirtatttu, wadanda kasar ce a zuciyarsu ba kawai abin da za su samu ba. Sannan, su kuma ‘yan kasa wajibi ne su zama masu yin zabe bisa akida ba don dan abin da za a ba su ba.

Alhaji Adamu Rabiu ya ruwaito da ga Kaduna

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INEC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Da Mata Za Su Bi Don Gyara Jikinsu

Next Post

Farashin Kayayyaki Ya Yi Tashin Gwauron Zabi A Birtaniya Saboda Tsadar Makamashi

Related

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

2 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

4 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

1 month ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

2 months ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

3 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

3 months ago
Next Post
Ya Kamata ‘Yan Siyasan Birtaniya Su Rika Yin Abu Gwargwadon Karfinsu

Farashin Kayayyaki Ya Yi Tashin Gwauron Zabi A Birtaniya Saboda Tsadar Makamashi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.