• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Ake Noma Tan  Miliyan 12.4 Kacal Na Masara A Wasu Sassan Nijeriya -Shugaba

byAbubakar Abba
2 years ago
Masara

Shugaban kungiyar manoman masara na kasa Dakta Bello Abubakar Funtua ya bayyana cewa, Masara tan miliyan 12.4 kacal aka iya noma wa kasar, sakamakon matsalolin ambaliyar a wasu sassa na kudu maso-gabas da kuma arewa maso gabas na kasar nan.

Bello ya sanar da hakan ne a wani taron kwararru a fannin na noman Masara da aka gudanar a kwanan baya, inda ya kara da cewa, kazalika  karancin taki a wasu sassa na yankankunan,  ya kara janyo rashin nomanta kamar yadda ake bukata.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Gwamnatin Jihar Gombe Na Bai Wa Fannin Noman Auduga  Mahimmanci – Kwamishina

“Tan miliyan 12.4 na Masara kacal aka iya noma wa a sakamakon matsalolin ambaliyar ruwa da karancin taki a wasu sassa na yankankunan kudu maso-gabas da kuma arewa ta gabas da arewa ta yamma.”

Ya ci gaba da cewa, a yanzu Nijeriya na samar da Masara ninki goma ne kawai, inda ya kara da cewa, daga 1999 zuwa shekara ta 2019, a duk shekara masarar da ake nomawa a Nijeriya ta na ninkawa sau biyu.

A cewarsa, hakan ya sanya daga 2014 zuwa 2019 Nijeriya ta zama kasa ta biyu kan noman Masara a Afrika, inda take noma Masara tan miliyan 10.8 a duk shekara baya ga Afrika ta Kudu wadda take kan gaba a noman Masara a nahiyar Afrika, da take noma masara tan miliyan 12.9 a duk shekara.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Bello, ya yi bayyana cewa shekara ta 2014 Nijeriya ta noma Masara tan miliyan 10.1 inda a 2015 ta noma tan miliyan 11.6, sai a 2016 da ta noma tan miliyan 11.6, sai shekarar 2017 ta noma tan miliyan 10.4, a 2018 zuwa 2019 ta noma kimanin tan miliyan 11.0.

” Daga 2014 zuwa 2019 Nijeriya ta zama kasa ta biyu kan noman Masara a Afrika, inda take noma Masara tan miliyan 10.8 a duk shekara baya ga Afrika ta Kudu wadda take kan gaba a noman Masara a nahiyar Afrika, da take noma masara tan miliyan 12.9 a duk shekara.”

Bello ya kuma buga misali da cewa, a shekaru biyar na tsohowar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Nijeriya tana noma masara tan miliyan 10.8 a duk shekara.

Ya bayyana cewa, Masarar da Nijeriya ta noma a shekara ta 2019 tan miliyan 12.6 ta yi kasa idan aka yi la’akari da wadda ta noma a shekarar 2020 a sakamakon matsalar karancin ruwan sama,

“Masarar da Nijeriya ta noma a shekara ta 2019 tan miliyan 12.6 ta yi kasa idan aka yi la’akari da wadda ta noma a shekarar 2020 a sakamakon matsalar karancin ruwan sama. ”

A na sa jawabin Darakta Janar na Majalisar samar da iri ta kasa Dakta  Philip Ojo, ya nanata mahimmancin akan shuka ingantacce Irin Masara, musamman domin manomanta su samu riba mai yawa.

Ya ce, ya zuwa yanzu an samar da irin shuka na masara daban-daban har 140, don ganin an bunkasa  noman Masara  a Nijeriya .

” Akwai matukar mahimmancin akan shuka ingantacce Irin Masara, musamman domin manomanta su samu riba mai yawa. ”

Shi kuwa wani kwararre a fannin  Mista Joseph Kibaki ya bayyana cewa, akwai bukatar a samar da kyawawan tsare -tsare da shirye shirye, musamman daga bangaren gwamnatin tarayya domin a kara bunkasa fannin noman Masara a daukacin fadin kasar nan.

“Akwai  bukatar a samar da kyawawan tsare -tsare da shirye shirye, musamman daga bangaren gwamnatin tarayya domin a kara bunkasa fannin noman Masara a daukacin fadin kasar nan.”

Su kuwa wasu masana a fannin noman Masara a kasar nan sun bayyana wasu hanyoyin da ya dace a dauka domin a kara bunkasa noman Masara a kasar nan.

Sun sanar da hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki a fannin suka gudanar tare da kuma kokarin lalubo da mafita kan kalubalen da fannin ke fuskanta.

Mahalarta taron sun kuma attaunawa kan kalubale da fannin ke fuskanta a kasar nan tare da kuma bayar da shawarwari, musamman ga gwamnatin tarayya kan yadda a lalubo da mafita akan kalubalen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version