• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Ake Noma Tan  Miliyan 12.4 Kacal Na Masara A Wasu Sassan Nijeriya -Shugaba

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilin Da Ya Sa Ake Noma Tan  Miliyan 12.4 Kacal Na Masara A Wasu Sassan Nijeriya -Shugaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar manoman masara na kasa Dakta Bello Abubakar Funtua ya bayyana cewa, Masara tan miliyan 12.4 kacal aka iya noma wa kasar, sakamakon matsalolin ambaliyar a wasu sassa na kudu maso-gabas da kuma arewa maso gabas na kasar nan.

Bello ya sanar da hakan ne a wani taron kwararru a fannin na noman Masara da aka gudanar a kwanan baya, inda ya kara da cewa, kazalika  karancin taki a wasu sassa na yankankunan,  ya kara janyo rashin nomanta kamar yadda ake bukata.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Gwamnatin Jihar Gombe Na Bai Wa Fannin Noman Auduga  Mahimmanci – Kwamishina

“Tan miliyan 12.4 na Masara kacal aka iya noma wa a sakamakon matsalolin ambaliyar ruwa da karancin taki a wasu sassa na yankankunan kudu maso-gabas da kuma arewa ta gabas da arewa ta yamma.”

Ya ci gaba da cewa, a yanzu Nijeriya na samar da Masara ninki goma ne kawai, inda ya kara da cewa, daga 1999 zuwa shekara ta 2019, a duk shekara masarar da ake nomawa a Nijeriya ta na ninkawa sau biyu.

A cewarsa, hakan ya sanya daga 2014 zuwa 2019 Nijeriya ta zama kasa ta biyu kan noman Masara a Afrika, inda take noma Masara tan miliyan 10.8 a duk shekara baya ga Afrika ta Kudu wadda take kan gaba a noman Masara a nahiyar Afrika, da take noma masara tan miliyan 12.9 a duk shekara.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

Bello, ya yi bayyana cewa shekara ta 2014 Nijeriya ta noma Masara tan miliyan 10.1 inda a 2015 ta noma tan miliyan 11.6, sai a 2016 da ta noma tan miliyan 11.6, sai shekarar 2017 ta noma tan miliyan 10.4, a 2018 zuwa 2019 ta noma kimanin tan miliyan 11.0.

” Daga 2014 zuwa 2019 Nijeriya ta zama kasa ta biyu kan noman Masara a Afrika, inda take noma Masara tan miliyan 10.8 a duk shekara baya ga Afrika ta Kudu wadda take kan gaba a noman Masara a nahiyar Afrika, da take noma masara tan miliyan 12.9 a duk shekara.”

Bello ya kuma buga misali da cewa, a shekaru biyar na tsohowar gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Nijeriya tana noma masara tan miliyan 10.8 a duk shekara.

Ya bayyana cewa, Masarar da Nijeriya ta noma a shekara ta 2019 tan miliyan 12.6 ta yi kasa idan aka yi la’akari da wadda ta noma a shekarar 2020 a sakamakon matsalar karancin ruwan sama,

“Masarar da Nijeriya ta noma a shekara ta 2019 tan miliyan 12.6 ta yi kasa idan aka yi la’akari da wadda ta noma a shekarar 2020 a sakamakon matsalar karancin ruwan sama. ”

A na sa jawabin Darakta Janar na Majalisar samar da iri ta kasa Dakta  Philip Ojo, ya nanata mahimmancin akan shuka ingantacce Irin Masara, musamman domin manomanta su samu riba mai yawa.

Ya ce, ya zuwa yanzu an samar da irin shuka na masara daban-daban har 140, don ganin an bunkasa  noman Masara  a Nijeriya .

” Akwai matukar mahimmancin akan shuka ingantacce Irin Masara, musamman domin manomanta su samu riba mai yawa. ”

Shi kuwa wani kwararre a fannin  Mista Joseph Kibaki ya bayyana cewa, akwai bukatar a samar da kyawawan tsare -tsare da shirye shirye, musamman daga bangaren gwamnatin tarayya domin a kara bunkasa fannin noman Masara a daukacin fadin kasar nan.

“Akwai  bukatar a samar da kyawawan tsare -tsare da shirye shirye, musamman daga bangaren gwamnatin tarayya domin a kara bunkasa fannin noman Masara a daukacin fadin kasar nan.”

Su kuwa wasu masana a fannin noman Masara a kasar nan sun bayyana wasu hanyoyin da ya dace a dauka domin a kara bunkasa noman Masara a kasar nan.

Sun sanar da hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki a fannin suka gudanar tare da kuma kokarin lalubo da mafita kan kalubalen da fannin ke fuskanta.

Mahalarta taron sun kuma attaunawa kan kalubale da fannin ke fuskanta a kasar nan tare da kuma bayar da shawarwari, musamman ga gwamnatin tarayya kan yadda a lalubo da mafita akan kalubalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noma
ShareTweetSendShare
Previous Post

UEFA Ta Wanke Barcelona Daga Zargin Kashe Kudi Ba Bisa Ka’ida Ba

Next Post

Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

6 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

7 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

Kasar Sweden Ta Yi Waje Rod Da Kasar Amurka A Gasar Cin Kofin Duniya Na Kwallon Mata

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.