• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

by Abubakar Abba
9 months ago
in Labarai, Noma Da Kiwo
0
Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu makiyaya a Jihar Taraba, sun tabka asarar Shanunsu sama da 1,000, sanadiyyar barkewar wata cuta a yankin Mambilla Filato da ke Karamar Hukumar Sardauna.

Rahotannin sun bayyana cewa, bullar wannan cuta; ita ce mafi muni a tarihin kiwo a yankin.

  • Gwamnan Filato Ya ƘaÆ™aba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • An Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Wani Artabu Da Sojoji A Filato

An ruwaito cewa, cutar wadda aka bayyana ta a matsayin mafi hadari ga Shanu, an fara gano bullar ta ne a Kauyukan Dorofi, Mayo Ndaga, Kwarakwara, Leme, Tep, Labare da kuma  Furmi a ranar 10 ga watan Yulin 2024.

Akasarin Fulani da sauran kabiliun da ke zaune a yankin na Mambilla Filato, makiyaya ne, wadanda ke killace Shanusu ba tare da barin su suna fita kiwo ba. An rawaito cewa, daya daga cikin masu kiwo a yankin; Alhaji Abbas Yabuba na cewa, wannan shi ne karo na biyu da masu kiwon suka yi asara a cikin kankanin lokaci na Shanu da dama sakamakon bullar wannan cuta.

Ya kara da cewa, a wannan karon cutar ta bulla ne a yankuna shida, ta kuma munana matuka; domin akwai mai kiwo daya, da ya yi asarar Shanu kimanin 80, sai kuma dai-daikun makiyaya da suka yi asarar Shanu daga 50 zuwa 60.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sai dai ya ce, daukin gaggawar da suka samu daga ma’aikatar aikin gona ta jihar, na zuwa duba lafiyar Shahun, ta taimaka matuka wajen dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani makiyayin, Adamu ya kiyasata asarar da masu kiwon suka yi sakamakon bullar cutar, inda ya ce ta haura sama da ta Naira biliyan uku.

Har ila yau, an ruwaito Daraktan duba lafiyar dabbobi na ma’aikatar aikin gona ta jihar, Dakta Francis Nathan ya sanar da cewa, an girke jami’an duba lafiyar dabbobi a shalkwatar Gembu ta Karamar Hukumar Sardauna, don kai wa ma’aikatar rahoton barkewar cutar.

Ya ci gaba da cewa, an samu magunguna da Allurai daga cibiyar binken lafiyar dabbobi ta kasa, Bom da ke Jihar Filato, don yi wa Shanun rigakafin cutar. Ya ce, sun yi hanzarin zuwa yankunnan da cutar ta barke tare da fara duba lafiyar Shanun da suka kamu da cutar, inda ya kara da cewa, Shanu sama da 500,000 aka duba lafiyarsu tare kuma da yi musu allurer rigakafi.

Har ila yau a cewar tasa, ana matukar samun shigowar makiyayan Shanu daga Kasar Kamaru zuwa cikin Karamar Hukumar Sardauna, haka nan mu ma namu na shiga kasar yin kiwo, inda ya sanar da cewa, dakatar da shigar Shanun ne kawai zai sa a dakile yaduwar cutar.

Haka zalika, wani bincike ya nuna cewa; duk da dimbin yawan dabbonin da ake da su a yankin na Mambilla Filato, duk dakin duba lafiyar dabbobi daya; likitan daya ne, duba da yadda aka kiyasata cewa, a Karamar Kukumar ta Sardauna akwai Shanu kimanin miliyan biyu da ake kiwatawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoNomaShanuTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin: An Samu Cikakkiyar Nasara A Taron FOCAC Na Shekara 2024

Next Post

An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

3 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

4 hours ago
Makiyaya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

9 hours ago
Next Post
An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Makiyaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.