• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

by Abubakar Abba
10 months ago
in Labarai, Noma Da Kiwo
0
Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu makiyaya a Jihar Taraba, sun tabka asarar Shanunsu sama da 1,000, sanadiyyar barkewar wata cuta a yankin Mambilla Filato da ke Karamar Hukumar Sardauna.

Rahotannin sun bayyana cewa, bullar wannan cuta; ita ce mafi muni a tarihin kiwo a yankin.

  • Gwamnan Filato Ya ƘaÆ™aba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • An Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Wani Artabu Da Sojoji A Filato

An ruwaito cewa, cutar wadda aka bayyana ta a matsayin mafi hadari ga Shanu, an fara gano bullar ta ne a Kauyukan Dorofi, Mayo Ndaga, Kwarakwara, Leme, Tep, Labare da kuma  Furmi a ranar 10 ga watan Yulin 2024.

Akasarin Fulani da sauran kabiliun da ke zaune a yankin na Mambilla Filato, makiyaya ne, wadanda ke killace Shanusu ba tare da barin su suna fita kiwo ba. An rawaito cewa, daya daga cikin masu kiwo a yankin; Alhaji Abbas Yabuba na cewa, wannan shi ne karo na biyu da masu kiwon suka yi asara a cikin kankanin lokaci na Shanu da dama sakamakon bullar wannan cuta.

Ya kara da cewa, a wannan karon cutar ta bulla ne a yankuna shida, ta kuma munana matuka; domin akwai mai kiwo daya, da ya yi asarar Shanu kimanin 80, sai kuma dai-daikun makiyaya da suka yi asarar Shanu daga 50 zuwa 60.

Labarai Masu Nasaba

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Sai dai ya ce, daukin gaggawar da suka samu daga ma’aikatar aikin gona ta jihar, na zuwa duba lafiyar Shahun, ta taimaka matuka wajen dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani makiyayin, Adamu ya kiyasata asarar da masu kiwon suka yi sakamakon bullar cutar, inda ya ce ta haura sama da ta Naira biliyan uku.

Har ila yau, an ruwaito Daraktan duba lafiyar dabbobi na ma’aikatar aikin gona ta jihar, Dakta Francis Nathan ya sanar da cewa, an girke jami’an duba lafiyar dabbobi a shalkwatar Gembu ta Karamar Hukumar Sardauna, don kai wa ma’aikatar rahoton barkewar cutar.

Ya ci gaba da cewa, an samu magunguna da Allurai daga cibiyar binken lafiyar dabbobi ta kasa, Bom da ke Jihar Filato, don yi wa Shanun rigakafin cutar. Ya ce, sun yi hanzarin zuwa yankunnan da cutar ta barke tare da fara duba lafiyar Shanun da suka kamu da cutar, inda ya kara da cewa, Shanu sama da 500,000 aka duba lafiyarsu tare kuma da yi musu allurer rigakafi.

Har ila yau a cewar tasa, ana matukar samun shigowar makiyayan Shanu daga Kasar Kamaru zuwa cikin Karamar Hukumar Sardauna, haka nan mu ma namu na shiga kasar yin kiwo, inda ya sanar da cewa, dakatar da shigar Shanun ne kawai zai sa a dakile yaduwar cutar.

Haka zalika, wani bincike ya nuna cewa; duk da dimbin yawan dabbonin da ake da su a yankin na Mambilla Filato, duk dakin duba lafiyar dabbobi daya; likitan daya ne, duba da yadda aka kiyasata cewa, a Karamar Kukumar ta Sardauna akwai Shanu kimanin miliyan biyu da ake kiwatawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoNomaShanuTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin: An Samu Cikakkiyar Nasara A Taron FOCAC Na Shekara 2024

Next Post

An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

Related

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

28 seconds ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

5 minutes ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

45 minutes ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

4 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Next Post
An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.