ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

by Abubakar Abba
2 years ago
Makiyaya

Wasu makiyaya a Jihar Taraba, sun tabka asarar Shanunsu sama da 1,000, sanadiyyar barkewar wata cuta a yankin Mambilla Filato da ke Karamar Hukumar Sardauna.

Rahotannin sun bayyana cewa, bullar wannan cuta; ita ce mafi muni a tarihin kiwo a yankin.

  • Gwamnan Filato Ya Ƙaƙaba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • An Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Wani Artabu Da Sojoji A Filato

An ruwaito cewa, cutar wadda aka bayyana ta a matsayin mafi hadari ga Shanu, an fara gano bullar ta ne a Kauyukan Dorofi, Mayo Ndaga, Kwarakwara, Leme, Tep, Labare da kuma  Furmi a ranar 10 ga watan Yulin 2024.

ADVERTISEMENT

Akasarin Fulani da sauran kabiliun da ke zaune a yankin na Mambilla Filato, makiyaya ne, wadanda ke killace Shanusu ba tare da barin su suna fita kiwo ba. An rawaito cewa, daya daga cikin masu kiwo a yankin; Alhaji Abbas Yabuba na cewa, wannan shi ne karo na biyu da masu kiwon suka yi asara a cikin kankanin lokaci na Shanu da dama sakamakon bullar wannan cuta.

Ya kara da cewa, a wannan karon cutar ta bulla ne a yankuna shida, ta kuma munana matuka; domin akwai mai kiwo daya, da ya yi asarar Shanu kimanin 80, sai kuma dai-daikun makiyaya da suka yi asarar Shanu daga 50 zuwa 60.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Sai dai ya ce, daukin gaggawar da suka samu daga ma’aikatar aikin gona ta jihar, na zuwa duba lafiyar Shahun, ta taimaka matuka wajen dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani makiyayin, Adamu ya kiyasata asarar da masu kiwon suka yi sakamakon bullar cutar, inda ya ce ta haura sama da ta Naira biliyan uku.

Har ila yau, an ruwaito Daraktan duba lafiyar dabbobi na ma’aikatar aikin gona ta jihar, Dakta Francis Nathan ya sanar da cewa, an girke jami’an duba lafiyar dabbobi a shalkwatar Gembu ta Karamar Hukumar Sardauna, don kai wa ma’aikatar rahoton barkewar cutar.

Ya ci gaba da cewa, an samu magunguna da Allurai daga cibiyar binken lafiyar dabbobi ta kasa, Bom da ke Jihar Filato, don yi wa Shanun rigakafin cutar. Ya ce, sun yi hanzarin zuwa yankunnan da cutar ta barke tare da fara duba lafiyar Shanun da suka kamu da cutar, inda ya kara da cewa, Shanu sama da 500,000 aka duba lafiyarsu tare kuma da yi musu allurer rigakafi.

Har ila yau a cewar tasa, ana matukar samun shigowar makiyayan Shanu daga Kasar Kamaru zuwa cikin Karamar Hukumar Sardauna, haka nan mu ma namu na shiga kasar yin kiwo, inda ya sanar da cewa, dakatar da shigar Shanun ne kawai zai sa a dakile yaduwar cutar.

Haka zalika, wani bincike ya nuna cewa; duk da dimbin yawan dabbonin da ake da su a yankin na Mambilla Filato, duk dakin duba lafiyar dabbobi daya; likitan daya ne, duba da yadda aka kiyasata cewa, a Karamar Kukumar ta Sardauna akwai Shanu kimanin miliyan biyu da ake kiwatawa.

Makiyaya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.