ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

by Abubakar Abba
2 years ago
Makiyaya

Wasu makiyaya a Jihar Taraba, sun tabka asarar Shanunsu sama da 1,000, sanadiyyar barkewar wata cuta a yankin Mambilla Filato da ke Karamar Hukumar Sardauna.

Rahotannin sun bayyana cewa, bullar wannan cuta; ita ce mafi muni a tarihin kiwo a yankin.

  • Gwamnan Filato Ya Ƙaƙaba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • An Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Wani Artabu Da Sojoji A Filato

An ruwaito cewa, cutar wadda aka bayyana ta a matsayin mafi hadari ga Shanu, an fara gano bullar ta ne a Kauyukan Dorofi, Mayo Ndaga, Kwarakwara, Leme, Tep, Labare da kuma  Furmi a ranar 10 ga watan Yulin 2024.

ADVERTISEMENT

Akasarin Fulani da sauran kabiliun da ke zaune a yankin na Mambilla Filato, makiyaya ne, wadanda ke killace Shanusu ba tare da barin su suna fita kiwo ba. An rawaito cewa, daya daga cikin masu kiwo a yankin; Alhaji Abbas Yabuba na cewa, wannan shi ne karo na biyu da masu kiwon suka yi asara a cikin kankanin lokaci na Shanu da dama sakamakon bullar wannan cuta.

Ya kara da cewa, a wannan karon cutar ta bulla ne a yankuna shida, ta kuma munana matuka; domin akwai mai kiwo daya, da ya yi asarar Shanu kimanin 80, sai kuma dai-daikun makiyaya da suka yi asarar Shanu daga 50 zuwa 60.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Sai dai ya ce, daukin gaggawar da suka samu daga ma’aikatar aikin gona ta jihar, na zuwa duba lafiyar Shahun, ta taimaka matuka wajen dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani makiyayin, Adamu ya kiyasata asarar da masu kiwon suka yi sakamakon bullar cutar, inda ya ce ta haura sama da ta Naira biliyan uku.

Har ila yau, an ruwaito Daraktan duba lafiyar dabbobi na ma’aikatar aikin gona ta jihar, Dakta Francis Nathan ya sanar da cewa, an girke jami’an duba lafiyar dabbobi a shalkwatar Gembu ta Karamar Hukumar Sardauna, don kai wa ma’aikatar rahoton barkewar cutar.

Ya ci gaba da cewa, an samu magunguna da Allurai daga cibiyar binken lafiyar dabbobi ta kasa, Bom da ke Jihar Filato, don yi wa Shanun rigakafin cutar. Ya ce, sun yi hanzarin zuwa yankunnan da cutar ta barke tare da fara duba lafiyar Shanun da suka kamu da cutar, inda ya kara da cewa, Shanu sama da 500,000 aka duba lafiyarsu tare kuma da yi musu allurer rigakafi.

Har ila yau a cewar tasa, ana matukar samun shigowar makiyayan Shanu daga Kasar Kamaru zuwa cikin Karamar Hukumar Sardauna, haka nan mu ma namu na shiga kasar yin kiwo, inda ya sanar da cewa, dakatar da shigar Shanun ne kawai zai sa a dakile yaduwar cutar.

Haka zalika, wani bincike ya nuna cewa; duk da dimbin yawan dabbonin da ake da su a yankin na Mambilla Filato, duk dakin duba lafiyar dabbobi daya; likitan daya ne, duba da yadda aka kiyasata cewa, a Karamar Kukumar ta Sardauna akwai Shanu kimanin miliyan biyu da ake kiwatawa.

Makiyaya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

An Zartas Da Hadaddiyar Sanarwa Game Da Zurfafa Hadin Gwiwa A Tsakanin Sin Da Afirka Bisa Tsarin Shawarar Ci Gaban Duniya A Taron Koli Na FOCAC

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.