• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Jonathan

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, a yau Alhamis ya bayyana cewa dakatar da tsohon Gwamnan babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammad Sanusi II, ya faru ne saboda wasu laifukan kuɗi ba don batun zargin batan kuɗi da yayi ba.

Jonathan ya bayyana hakan ne a Abuja yayin ƙaddamar da wani littafi da tsohon Ministan Kudi, Dr. Shamsudeen Usman, ya rubuta mai suna “Public Policy and Agent Interests: Perspectives from the Emerging World.”

  • EFCC Ba Ta Taba Gayyato Ni Gabanta Ba – Jonathan
  • Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan

Jonathan ya musanta ikirarin Muhammadu Sanusi na cewa an dakatar da shi ne saboda ya fallasa zargin batan $49.8 biliyan daga asusun gwamnatin tarayya. Ya yi bayanin cewa an dakatar da Sanusi ne bayan tambayar da kwamitin rahoton kudi na Nijeriya (FRC) ya yi kan wasu kashe-kuɗaɗen da ba su dace ba a CBN. Jonathan ya ƙara da cewa, “Akwai matsalolin da suka dace a bincika.”

Tsohon shugaban ya kuma musanta zargin cewa Nijeriya ta rasa wannan adadin kuɗin a lokacin mulkinsa, yana mai cewa kasafin kuɗin ƙasar a wancan lokacin bai wuce ya kai $31.6 biliyan ba kawai, don haka ba zai yiwu a ce $49.8 biliyan sun bace ba tare da an lura ba.

Jonathan ya jaddada cewa bayan binciken kuɗi na PwC, an gano cewa $1.48 biliyan ne ba a bayyana ba, kuma an umurci kamfanin NNPC da ya biya wannan kuɗin cikin Asusun Tarayya. Ya kuma bayyana cewa binciken majalisar dattijai bai gano shaidar batan miliyoyin kuɗaɗen da ake zargi ba.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Sanusi, wanda ya halarci taron, ya mayar da martani cikin raha, inda ya kira Jonathan da “Ogana wanda ya kore Ni,” amma Khalifa ya zaɓi ƙin yin tsokaci kan batun. Maimakon haka, ya ja hankalin ƙasar kan amfani da Matatar man fetur ta Dangote yadda ya kamata tare da kauce wa duk wani cikas ga ci gabanta.

An kuma ƙaddamar da Cibiyar Shamsudeen Usman Foundation da kuma wani taron neman taimakon kuɗi don ƙirƙirar Cibiyar Fasahar Artificial Intelligence a yayin taron.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
Manyan Labarai

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
Next Post
Zamfara

Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta'addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.