• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, a yau Alhamis ya bayyana cewa dakatar da tsohon Gwamnan babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammad Sanusi II, ya faru ne saboda wasu laifukan kuɗi ba don batun zargin batan kuɗi da yayi ba.

Jonathan ya bayyana hakan ne a Abuja yayin ƙaddamar da wani littafi da tsohon Ministan Kudi, Dr. Shamsudeen Usman, ya rubuta mai suna “Public Policy and Agent Interests: Perspectives from the Emerging World.”

  • EFCC Ba Ta Taba Gayyato Ni Gabanta Ba – Jonathan
  • Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan

Jonathan ya musanta ikirarin Muhammadu Sanusi na cewa an dakatar da shi ne saboda ya fallasa zargin batan $49.8 biliyan daga asusun gwamnatin tarayya. Ya yi bayanin cewa an dakatar da Sanusi ne bayan tambayar da kwamitin rahoton kudi na Nijeriya (FRC) ya yi kan wasu kashe-kuɗaɗen da ba su dace ba a CBN. Jonathan ya ƙara da cewa, “Akwai matsalolin da suka dace a bincika.”

Tsohon shugaban ya kuma musanta zargin cewa Nijeriya ta rasa wannan adadin kuɗin a lokacin mulkinsa, yana mai cewa kasafin kuɗin ƙasar a wancan lokacin bai wuce ya kai $31.6 biliyan ba kawai, don haka ba zai yiwu a ce $49.8 biliyan sun bace ba tare da an lura ba.

Jonathan ya jaddada cewa bayan binciken kuɗi na PwC, an gano cewa $1.48 biliyan ne ba a bayyana ba, kuma an umurci kamfanin NNPC da ya biya wannan kuɗin cikin Asusun Tarayya. Ya kuma bayyana cewa binciken majalisar dattijai bai gano shaidar batan miliyoyin kuɗaɗen da ake zargi ba.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Sanusi, wanda ya halarci taron, ya mayar da martani cikin raha, inda ya kira Jonathan da “Ogana wanda ya kore Ni,” amma Khalifa ya zaɓi ƙin yin tsokaci kan batun. Maimakon haka, ya ja hankalin ƙasar kan amfani da Matatar man fetur ta Dangote yadda ya kamata tare da kauce wa duk wani cikas ga ci gabanta.

An kuma ƙaddamar da Cibiyar Shamsudeen Usman Foundation da kuma wani taron neman taimakon kuɗi don ƙirƙirar Cibiyar Fasahar Artificial Intelligence a yayin taron.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JonathanMuhammadu Sunusi IIShamsuddeen Muhammad
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da Lardin Jiangsu Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Ta Tallata Tamburar Hajojin Lardin

Next Post

Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta’addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

Related

Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

7 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

13 hours ago
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta
Manyan Labarai

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

13 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

2 days ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

2 days ago
Next Post
Zamfara

Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta'addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.