• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

by Sadiq
4 months ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa mai kula da yankin Arewa maso Gabas, Mustapha Salihu, ya bayyana dalilin da ya sa ya mara wa Shugaba Bola Tinubu baya domin sake tsayawa takara a 2027 ba tare da ambaton Mataimakin Shugaba Ƙasa, Kashim Shettima, a jawabinsa ba. 

Jawabin nasa ya janyo ce-ce-ku-ce a taron shugabannin APC na Arewa maso Gabas da aka yi a Jihar Gombe.

  • ‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Salihu ya ce ba a fahimce shi ba ne, kuma kafafen yaɗa labarai sun bayar da rahoton ba daidai ba.

“Wannan matsala ta faru ne saboda yadda aka yi wa jawabina fassara ba daidai ba. Da an saurari jawabin gaba ɗaya, musamman ƙarshensa, da an ji na yaba wa Mataimakin Shugaban Ƙasa,” in ji shi.

Salihu ya ce kafin ya nemi a goyi bayan Tinubu ya sake tsayawa takara, ya fara da yaba wa Shettima da sauran ‘yan yankin Arewa maso Gabas da aka ba su manyan muƙamai a gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

“Na ce Shettima ɗanmu ne, kuma muna alfahari da shi. Na kuma gode wa Tinubu bisa yadda ya bai wa ‘yan Arewa maso Gabas muƙamai masu gwaɓi kafin na nemi a mara masa baya,” in ji Salihu.

A lokacin taron, wasu matasa sun kusan kai masa hari, amma ya ce hakan ya faru ne saboda wasu ba su fahimci abin da ya yi ba.

Ya kuma jaddada cewa a tsarin jam’iyya, mutum ɗaya ne kawai ake zaɓa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a lokacin zaɓen fidda gwani, kuma shi ne ke da ‘yancin zaɓar mataimakinsa.

“Ba a daidaita tikitin shugaba da mataimaki a zaɓen fidda gwani. Ɗan takara kawai ake zaɓa, kuma yana da ‘yancin zaɓar wanda zai mara masa baya,” in ji shi.

Salihu ya kuma ƙaryata jita-jitar cewa akwai saɓani tsakanin Tinubu da Shettima.

Ya zargi wasu da ya kira “’yan kasuwar rikici” da ƙoƙarin ɓata lamarin domin amfanin kansu.

“Waɗanda ke yaɗa irin waɗannan labarai suna neman cin moriyar rikicin ne. Ba a gudanar da harkokin jam’iyya a dandalin sada zumunta ko a jaridu ba, a ofishin jam’iyya ake yin hakan,” in ji shi.

A ƙarshe, Salihu ya roƙi mambobin jam’iyyar da al’umma su guji yarda da jita-jita, yana mai cewa jam’iyyar APC na nan daram, babu wata matsala.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCArewa Maso GabasSalihuShettimaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Next Post

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

18 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.