• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Tashin Farashin Wake A Nijeriya

by Abubakar Abba
11 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsadar farashin Wake, ya jefa fargaba a zukatan mutane da dama a Nijeriya; wanda har yanzu ke ci gaba da haifar da cece-kuce.

An ruwaito cewa, tashin farashin Waken na kokarin wuce gona da iri, wanda a tarihi ba a taba ganin irinsa a fadin wannan kasa ba.

  • Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa
  • Akwai Bukatar Mu Bai Wa Mara Ɗa Kunya A Gasar EURO Ta Bana – Gordon

Har ila yau, manoman sun danganta wannan tsada tasa a kan abubuwa da dama da suka shafi nomansa a Nijeriya.

Kungiyar Manoman Farin Wake ta Kasa (CFAN), ta sanar da cewa; ana daukar mataki don lalubo mafita a kan wannan hauhawar farashi a fadin wannan kasa.

Shugaban kungiyar na kasa reshen Jihar Kano, Malam Sale Maigari Tunfafi ya sanar da cewa, ba Wake kadai wannan hauhawar farashi ya shafa ba, sai dai kawai tashin farashin Waken ne ya fi munana.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Ya sanar da cewa, daya daga cikin abin da ya jawo tsadar shi ne; raguwar da aka samu ta masu yin nomansa a bara, inda ya yi nuni da cewa, Wake na daya daga cikin amfanin gona da ake girbewa a duk shekara.

Ya kara da cewa, kutsawar da Fulani Makiyaya ke yi cikin gonakin da aka yi shuka, na haifar da lalacewar amfanin da aka shuka.

Kazalika, ya danganta hauhawar farashin kayan nomansa; wanda ya jawo aka samu raguwar yawan masu yin nomansa a fadin wannan kasa.

Ya ci gaba da cewa, shigo da Waken da wasu manyan dillalansa ke yi daga makwabtan kasashen Nijieriya, ya kara haifar da wannan hauhawar farashi nasa a wannan kasa.

A cewarsa, fadauwar darajar Naira; ita ma ta taimaka wajen haifar da tashin farashin nasa, wanda hakan ya sa wasu manyan dillalansa ke fitar da shi zuwa wasu kasashe, domin samun kudin musaya da kuma kazamar riba.

Ya bayyana cewa, tuni sun fara daukar matakai; domin noma Waken da yawa, wanda hakan zai sa tsadar tasa ta ragu.

Rahotannin sun yi nuni da cewa, farashin nasa ya haura Naira 200,000 duk loka daya, wanda ake ganin shi ne mafi munin tashin farashinsa a shekaru da dama da suka gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: TsadaWake
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

Next Post

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

13 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

20 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.