ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka: Yabon Gwani Ya Zama Dole

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Kasashen Afrika na kara samun ci gaba da kara amfana daga kyakkaywar dangantakar moriyar juna dake tsakaninsu da kasar Sin.

A wannan mako, kasar Habasha ta kaddamar da manyan ayyukan ci gaba guda biyu masu muhimmanci ga tattalin arziki da walwalar jama’a da suka hada da yankin ciniki cikin ’yanci na farko a kasar da kuma wani babban titin da ya fara daga shataletalen Alexander Puskin zuwa babban titin Gotera, dake birnin Addis Ababa.

  • Sharhi: Afirka Wani Babban Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Ne Ba Fagen Takara Tsakanin Manyan Kasashe Ba

A ko da yaushe, na kan ce dangantakar Sin da kasashen Afrika dangantaka ce ta zahiri da idanu ke iya gani, sannan al’umma kan amfana kai tsaye.

ADVERTISEMENT

Yankin masana’antu na Dire Dawa da tashar jiragen ruwa ta kan tudu da tashar jirgin kasa da ta hada Habasha da Djibouti ne suka hade, suka zama yankin na ciniki cikin ’yanci.

Dukkan wadannan ayyuka ne da Sin ke da ruwa da tsaki wajen wanzuwarsu, wadanda kuma kasar za ta dade tana cin gajiyarsu.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Yankin masana’antu na Dire Dawa kadai, zai taimaka wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye da wanda ba na kai tsaye ba ga al’ummar kasar 40,000, baya ga wadanda ya samarwa aikin yi yayin da ake gininsa.

Wannan yankin da ba za a taba raba nasararsa da taimakon kasar Sin ba, zai yi gagarumin taimako wajen habaka cinikayya tsakanin kasar da sauran kasashen Afrika musamman na gabashin nahiyar da saukaka jigilar kayayyaki da inganta rayuwar mazauna yankin da ma kai kasar ga cimma burinta na zama kasa mai matsakaicin kudin shiga zuwa shekarar 2025.

Kasar Habasha ta tsara burinta na zama cibiyar samar da kayayyaki da masana’antu na zamani a nahiyar Afrika, kuma kasar Sin tana iya kokarinta na ganin ta cimma wannan buri.

Har ila yau a jiya, kasar ta kaddamar da babban titin da ya fara daga shataletalen Alexander Puskin zuwa babban titin Gotera, a birnin Addis Ababa.

Titi muhimmin aikin more rayuwar al’umma ne domin zirga-zirga ya shafi dukkan bangarorin rayuwa, kama daga zuwa aiki, asibiti, jigilar kayayyakin bukata, da dai sauransu.

Tabbas kasar Sin ta cancanci yabo. Hakika duk wanda zai soki dangantakar Sin da Afrika, to ba ya kaunar ganin ci gaban kasashen na Afrika, domin cikin lokaci kalilan da aka dauka na dangantakar bangarorin biyu, an samu dimbin nasarorin da suka amfanawa daukacin al’umma, wadanda tarin zuri’a masu zuwa, su ma za su ci gajiya.(Fa’iza Mustapha)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana

Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.