• Leadership Hausa
Thursday, September 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka: Yabon Gwani Ya Zama Dole

by CMG Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Dangantakar Sin Da Kasashen Afirka: Yabon Gwani Ya Zama Dole
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen Afrika na kara samun ci gaba da kara amfana daga kyakkaywar dangantakar moriyar juna dake tsakaninsu da kasar Sin.

A wannan mako, kasar Habasha ta kaddamar da manyan ayyukan ci gaba guda biyu masu muhimmanci ga tattalin arziki da walwalar jama’a da suka hada da yankin ciniki cikin ’yanci na farko a kasar da kuma wani babban titin da ya fara daga shataletalen Alexander Puskin zuwa babban titin Gotera, dake birnin Addis Ababa.

  • Sharhi: Afirka Wani Babban Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Ne Ba Fagen Takara Tsakanin Manyan Kasashe Ba

A ko da yaushe, na kan ce dangantakar Sin da kasashen Afrika dangantaka ce ta zahiri da idanu ke iya gani, sannan al’umma kan amfana kai tsaye.

Yankin masana’antu na Dire Dawa da tashar jiragen ruwa ta kan tudu da tashar jirgin kasa da ta hada Habasha da Djibouti ne suka hade, suka zama yankin na ciniki cikin ’yanci.

Dukkan wadannan ayyuka ne da Sin ke da ruwa da tsaki wajen wanzuwarsu, wadanda kuma kasar za ta dade tana cin gajiyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Yankin masana’antu na Dire Dawa kadai, zai taimaka wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye da wanda ba na kai tsaye ba ga al’ummar kasar 40,000, baya ga wadanda ya samarwa aikin yi yayin da ake gininsa.

Wannan yankin da ba za a taba raba nasararsa da taimakon kasar Sin ba, zai yi gagarumin taimako wajen habaka cinikayya tsakanin kasar da sauran kasashen Afrika musamman na gabashin nahiyar da saukaka jigilar kayayyaki da inganta rayuwar mazauna yankin da ma kai kasar ga cimma burinta na zama kasa mai matsakaicin kudin shiga zuwa shekarar 2025.

Kasar Habasha ta tsara burinta na zama cibiyar samar da kayayyaki da masana’antu na zamani a nahiyar Afrika, kuma kasar Sin tana iya kokarinta na ganin ta cimma wannan buri.

Har ila yau a jiya, kasar ta kaddamar da babban titin da ya fara daga shataletalen Alexander Puskin zuwa babban titin Gotera, a birnin Addis Ababa.

Titi muhimmin aikin more rayuwar al’umma ne domin zirga-zirga ya shafi dukkan bangarorin rayuwa, kama daga zuwa aiki, asibiti, jigilar kayayyakin bukata, da dai sauransu.

Tabbas kasar Sin ta cancanci yabo. Hakika duk wanda zai soki dangantakar Sin da Afrika, to ba ya kaunar ganin ci gaban kasashen na Afrika, domin cikin lokaci kalilan da aka dauka na dangantakar bangarorin biyu, an samu dimbin nasarorin da suka amfanawa daukacin al’umma, wadanda tarin zuri’a masu zuwa, su ma za su ci gajiya.(Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Tsaro: Sojoji Sun Sake Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda A Kaduna 

Next Post

Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana

Related

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

21 mins ago
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

1 hour ago
Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba
Daga Birnin Sin

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

2 hours ago
Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

3 hours ago
Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

5 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

5 hours ago
Next Post
Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana

Wani Mutum Ya Yanke Marainansa Yana Barci, Ya Dauka Nama Ne A Ghana

LABARAI MASU NASABA

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

September 21, 2023
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

September 21, 2023
Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

September 21, 2023
Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

September 21, 2023
Super Eagles Ta Nijeriya Ta Dawo Mataki Na 40 A Jadawalin Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

Super Eagles Ta Nijeriya Ta Dawo Mataki Na 40 A Jadawalin Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

September 21, 2023
Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

September 21, 2023
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

September 21, 2023
Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

September 21, 2023
IPC

IPC Ta Yi Tir Da Muzguna Wa ‘Yan Jarida Yayin Daukan Rahoton Shari’ar Kujerar Gwamna A Kano

September 21, 2023
Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

September 21, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.