• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Sharhi: Afirka Wani Babban Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Ne Ba Fagen Takara Tsakanin Manyan Kasashe Ba

by CMG Hausa
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Afirka Wani Babban Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Ne Ba Fagen Takara Tsakanin Manyan Kasashe Ba

Kwanan nan, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya kawo karshen ziyararsa a wasu kasashen Afirka guda uku.

A yayin ziyararsa a kasar Afirka ta kudu, Mr.Blinken ya gabatar da jawabi dangane da sabbin tsare-tsaren kasar Amurka a kan Afirka, inda ya furta cewa, duk da ja-in-jan da ke kara ta’azzara a tsakanin Amurka da sauran manyan kasashen irinsu Sin da Rasha, Amurka dai ba za ta bukaci kasashen Afirka su zabi wani matsayin da za su dauka ba. Duk da haka, Blinken ya yi ta furta “barazanar” da Sin da Rasha ke haifarwa a kalamansa.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Sai dai tuni bangarori daban daban a kasashen Afirka sun gane ainihin abin da Mr. Blinken ke neman cimmawa.

Don haka, a yayin da take ganawa da manema labarai tare da Mr.Blinken, ministar harkokin wajen kasar Afirka ta kudu Naledi Pandor ta jaddada cewa, kasashen Afirka suna da ‘yancin kulla da kuma bunkasa hulda da mabambantan kasashe.

Kafofin yada labarai da masana na Afirka ma sun soki sabbin tsare-tsaren kasar Amurka a kan Afirka, ganin yadda take yin amfani da kasashen Afirka wajen yin takara da manyan kasashe, a maimakon kawo wata moriya ga kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sun kuma yi nuni da cewa, “sabon cacar baka” wani tarko ne da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke yunkurin danawa, amma kasashen Afirka ba sa so su zabi wani matsayin da za su dauka ba.

A hakika, kasashen duniya na zaman cude-ni-in-cude-ka ne, kuma makomarsu daya ce. Sai dai abin bakin ciki shi ne, Amurka wadda ra’ayin babakere da nuna fin karfi ya zame mata jiki, ta fi karkata ne kawai ga takara a wannan duniya, a maimakon hadin gwiwar cin moriyar juna.

Sabo da haka, Amurka ta kasa fahimtar irin zumunta da hadin gwiwa da ke tsakanin Sin da Afirka, kasancewarsu kasashe masu tasowa ne duka, baya ga manufar makomar bai daya ga dukkanin ‘yan Adam da kasar Sin ta gabatar.

A yayin ziyararsa Nijeriya a farkon shekarar bara, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi nuni da cewa, Afirka wani babban dandalin hadin gwiwar kasa da kasa ne ba fagen takara tsakanin manyan kasashe ba. Alkawari ne da kasar Sin ta dauka, kuma kasar ta cika.

Duk da zancen “barazanar kasar Sin” da Amurka ke kokarin yayatawa, ba za a iya kawar da kai daga nasarorin da kasashen Sin da Afirka suka cimma a hadin gwiwarsu ba. Hanyoyin jirgin kasa, da titunan mota, da tashoshin jiragen ruwa, da manyan gine-ginen da kasar Sin ta taimaka wajen ginawa a Afirka, duk suna nan a zahiri, wadanda kuma suke amfanar al’ummun kasashen a zahiri.

Kasashen Afirka ba sa bukatar aminiya wadda za ta rika jirkita gaskiya, kuma idanun ‘yan Afirka a bude suke. In dai da gaske Amurka tana son taimakawa nahiyar Afirka, ya dace ta dauki matakan zahiri, maimakon ta yi amfani da manyan tsare-tsarenta kan nahiyar Afirka, don hana ci gaban hadin-gwiwar Afirka da wasu kasashe. (Mustapha Bulama)

Previous Post

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutane 50, Da Dama Sun Rasa Muhallansu A Jigawa

Next Post

Abin Da Ya Faru Da Ni Daga Allah Ne Ban Zargin Kowa -Nasiru Soja

Related

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca
Daga Birnin Sin

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

17 hours ago
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

18 hours ago
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka
Daga Birnin Sin

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

21 hours ago
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

21 hours ago
Mataimakin Firayin Ministan Thailand: Sake Fara Ziyarar Sinawa Masu Yawon Shakatawa A Thailand Na Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firayin Ministan Thailand: Sake Fara Ziyarar Sinawa Masu Yawon Shakatawa A Thailand Na Da Babbar Ma’ana

1 day ago
IMF: Tattalin Arzikin Sin Na Bayar Da Gudunmuwa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

IMF: Tattalin Arzikin Sin Na Bayar Da Gudunmuwa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

1 day ago
Next Post
Abin Da Ya Faru Da Ni Daga Allah Ne Ban Zargin Kowa -Nasiru Soja

Abin Da Ya Faru Da Ni Daga Allah Ne Ban Zargin Kowa -Nasiru Soja

LABARAI MASU NASABA

Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano

Ya Uwargida Za Ta Yi Da Mijin Da Bai Iya Zaman Hira Ba?

February 6, 2023
Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina

Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina

February 6, 2023
Gwamnonin Kaduna, Kogi Da Zamfara Sun Maka Gwamnati A Kotu Kan Karancin Kudi

Gwamnonin Kaduna, Kogi Da Zamfara Sun Maka Gwamnati A Kotu Kan Karancin Kudi

February 6, 2023
Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar APC A Yobe Ta Arewa

February 6, 2023
PDP Ta Zargi Tinubu Da APC Kan Boye Sabbin Kudi Don Sayen Kuri’u

PDP Ta Zargi Tinubu Da APC Kan Boye Sabbin Kudi Don Sayen Kuri’u

February 6, 2023
Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

Kwalliyar Doguwar Rigar Abaya

February 6, 2023
2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

February 6, 2023
2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

February 6, 2023
Tashoshin Talabijin 6 Zasu Haska Shiri Na Musanman Kan Rayuwar Shugaba Buhari

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

February 6, 2023
Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.