ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Afirka Wani Babban Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Ne Ba Fagen Takara Tsakanin Manyan Kasashe Ba

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Kwanan nan, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya kawo karshen ziyararsa a wasu kasashen Afirka guda uku.

A yayin ziyararsa a kasar Afirka ta kudu, Mr.Blinken ya gabatar da jawabi dangane da sabbin tsare-tsaren kasar Amurka a kan Afirka, inda ya furta cewa, duk da ja-in-jan da ke kara ta’azzara a tsakanin Amurka da sauran manyan kasashen irinsu Sin da Rasha, Amurka dai ba za ta bukaci kasashen Afirka su zabi wani matsayin da za su dauka ba. Duk da haka, Blinken ya yi ta furta “barazanar” da Sin da Rasha ke haifarwa a kalamansa.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Sai dai tuni bangarori daban daban a kasashen Afirka sun gane ainihin abin da Mr. Blinken ke neman cimmawa.

ADVERTISEMENT

Don haka, a yayin da take ganawa da manema labarai tare da Mr.Blinken, ministar harkokin wajen kasar Afirka ta kudu Naledi Pandor ta jaddada cewa, kasashen Afirka suna da ‘yancin kulla da kuma bunkasa hulda da mabambantan kasashe.

Kafofin yada labarai da masana na Afirka ma sun soki sabbin tsare-tsaren kasar Amurka a kan Afirka, ganin yadda take yin amfani da kasashen Afirka wajen yin takara da manyan kasashe, a maimakon kawo wata moriya ga kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sun kuma yi nuni da cewa, “sabon cacar baka” wani tarko ne da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke yunkurin danawa, amma kasashen Afirka ba sa so su zabi wani matsayin da za su dauka ba.

A hakika, kasashen duniya na zaman cude-ni-in-cude-ka ne, kuma makomarsu daya ce. Sai dai abin bakin ciki shi ne, Amurka wadda ra’ayin babakere da nuna fin karfi ya zame mata jiki, ta fi karkata ne kawai ga takara a wannan duniya, a maimakon hadin gwiwar cin moriyar juna.

Sabo da haka, Amurka ta kasa fahimtar irin zumunta da hadin gwiwa da ke tsakanin Sin da Afirka, kasancewarsu kasashe masu tasowa ne duka, baya ga manufar makomar bai daya ga dukkanin ‘yan Adam da kasar Sin ta gabatar.

A yayin ziyararsa Nijeriya a farkon shekarar bara, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi nuni da cewa, Afirka wani babban dandalin hadin gwiwar kasa da kasa ne ba fagen takara tsakanin manyan kasashe ba. Alkawari ne da kasar Sin ta dauka, kuma kasar ta cika.

Duk da zancen “barazanar kasar Sin” da Amurka ke kokarin yayatawa, ba za a iya kawar da kai daga nasarorin da kasashen Sin da Afirka suka cimma a hadin gwiwarsu ba. Hanyoyin jirgin kasa, da titunan mota, da tashoshin jiragen ruwa, da manyan gine-ginen da kasar Sin ta taimaka wajen ginawa a Afirka, duk suna nan a zahiri, wadanda kuma suke amfanar al’ummun kasashen a zahiri.

Kasashen Afirka ba sa bukatar aminiya wadda za ta rika jirkita gaskiya, kuma idanun ‘yan Afirka a bude suke. In dai da gaske Amurka tana son taimakawa nahiyar Afirka, ya dace ta dauki matakan zahiri, maimakon ta yi amfani da manyan tsare-tsarenta kan nahiyar Afirka, don hana ci gaban hadin-gwiwar Afirka da wasu kasashe. (Mustapha Bulama)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Abin Da Ya Faru Da Ni Daga Allah Ne Ban Zargin Kowa -Nasiru Soja

Abin Da Ya Faru Da Ni Daga Allah Ne Ban Zargin Kowa -Nasiru Soja

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.