• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

by Bello Hamza
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Dangote ya musanta labarin da ya karade kakafen yada labarin da ke nuni da cewa kamfanin mai na kasa ya kinkimo bashin dala biliyan guda domin tallafa wa matatan man Dangote.

Dangote ya musanta labarin ne cikin wata sanarwa wanda mai magana da yawun kamfanin, Anthony Chiejina ya fitar a ranar Laraba.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Isa Yankin Macao
  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 

Sanarwar ta ce, “Mun samu tambayoyi da dama daga kafafen yada labarai da sauran masu ruwa da tsaki da ke neman qarin haske kan wani rahoto na baya-bayan nan da aka danganta ga kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), cewa matakin da suka dauka na samun lamuni na dala biliyan 1 daga danyen mai na tallafa wa matatar ta Dangote a lokacin da ya fuskanci kalubalen ba gaskiya ba ne.

 

“Muna so mu fayyace cewa wannan kuskure ne na lamari, domin dala biliyan 1 kusan kashi 5 ne na jarin aka kashe wajen gina matatar Dangote.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

“Shawarar da muka yanke na kulla kawance da NNPCL ya ta’allaka ne kan amincewa da dabarunsu a masana’antar a matsayinsu na masu safarar danyen man fetur mafi girma a Nijeriya a wannan lokacin, su ne kadai suke samar da man fetur a Nijeriya.

“Mun amince kan sayar da hannun jarin kashi 20, kan darajar dala biliyan 2.76. Daga cikin wannan, mun amince da cewa za su biya dala biliyan 1 ne kawai yayin da za a kwato ma’auni na tsawon shekaru 5 ta hanyar cire mana danyen mai da suke kawo mana da kuma ribar da ake samu. Idan da muna cikin kalubalen kudi da ba mu ba su irin wadannan sharuddan biyan kudi masu yawa ba. Kamar yadda a 2021, lokacin da aka sanya hannu kan yarjejeniyar, matatar ta kasance a matakin farko. Bugu da kari, da a ce muna da matsalar kudi, da wannan yarjejeniya ta kasance an biya tsabar kudin nan take.

“Sai dai kuma abin takaicin shi ne, daga baya kamfanin na NNPC ya kasa samar da ganga dubu 300 da aka amince da shi a rana na danyen mai ganin cewa sun sadaukar da mafi yawa daga cikin danyen da suka samu ga masu kudi tare da fatan samun karin hako mai wanda suka kasa cimma ruwa.

“Daga nan kuma muka ba su wa’adin watanni 12 domin su biya cikon kudadensu ganin yadda suka kasa samar da adadin danyen mai da aka amince da su. Kamfanin NNPCL ya gaza cika wannan wa’adin da ya kare a ranar 30 ga watan Yunin 2024. Sakamakon haka, an sake bitar kason su zuwa kashi 7.24. Dukkan bangarorin biyu sun ba da rahoton wadannan abubuwan da suka faru.

“Don haka, ba daidai ba ne a yi ikirarin cewa NNPCL ya ciyo bashin dala biliyan 1 domin tallafa wa matatar man Dangote. Kamar duk abokan huldar kasuwanci, NNPCL ya zuba jarin dala biliyan 1 a matatar man domin samun hannun jarin na kashi 7.24 wanda zai amfanar da muradunta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta qara da cewa Kamfanin NNPCPL ya kasance abokin hulda mai kima wajen samun ci gaba, kuma ya zama wajibi ga duk masu ruwa da tsaki su kiyaye gaskiya tare da gabatar da sahihin labari, don jagorantar kafafen yada labarai wajen bayar da sahihin rahoto wanda zai amfanin masu ruwa da tsaki da daukaci al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiDangoteLabariMatataNNPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Jinping Ya Isa Yankin Macao

Next Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

6 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

8 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

16 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

1 day ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

1 day ago
Next Post
Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Dangote

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.