• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

by Bello Hamza
10 months ago
Dangote

Kamfanin Dangote ya musanta labarin da ya karade kakafen yada labarin da ke nuni da cewa kamfanin mai na kasa ya kinkimo bashin dala biliyan guda domin tallafa wa matatan man Dangote.

Dangote ya musanta labarin ne cikin wata sanarwa wanda mai magana da yawun kamfanin, Anthony Chiejina ya fitar a ranar Laraba.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Isa Yankin Macao
  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 

Sanarwar ta ce, “Mun samu tambayoyi da dama daga kafafen yada labarai da sauran masu ruwa da tsaki da ke neman qarin haske kan wani rahoto na baya-bayan nan da aka danganta ga kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), cewa matakin da suka dauka na samun lamuni na dala biliyan 1 daga danyen mai na tallafa wa matatar ta Dangote a lokacin da ya fuskanci kalubalen ba gaskiya ba ne.

 

“Muna so mu fayyace cewa wannan kuskure ne na lamari, domin dala biliyan 1 kusan kashi 5 ne na jarin aka kashe wajen gina matatar Dangote.

LABARAI MASU NASABA

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

“Shawarar da muka yanke na kulla kawance da NNPCL ya ta’allaka ne kan amincewa da dabarunsu a masana’antar a matsayinsu na masu safarar danyen man fetur mafi girma a Nijeriya a wannan lokacin, su ne kadai suke samar da man fetur a Nijeriya.

“Mun amince kan sayar da hannun jarin kashi 20, kan darajar dala biliyan 2.76. Daga cikin wannan, mun amince da cewa za su biya dala biliyan 1 ne kawai yayin da za a kwato ma’auni na tsawon shekaru 5 ta hanyar cire mana danyen mai da suke kawo mana da kuma ribar da ake samu. Idan da muna cikin kalubalen kudi da ba mu ba su irin wadannan sharuddan biyan kudi masu yawa ba. Kamar yadda a 2021, lokacin da aka sanya hannu kan yarjejeniyar, matatar ta kasance a matakin farko. Bugu da kari, da a ce muna da matsalar kudi, da wannan yarjejeniya ta kasance an biya tsabar kudin nan take.

“Sai dai kuma abin takaicin shi ne, daga baya kamfanin na NNPC ya kasa samar da ganga dubu 300 da aka amince da shi a rana na danyen mai ganin cewa sun sadaukar da mafi yawa daga cikin danyen da suka samu ga masu kudi tare da fatan samun karin hako mai wanda suka kasa cimma ruwa.

“Daga nan kuma muka ba su wa’adin watanni 12 domin su biya cikon kudadensu ganin yadda suka kasa samar da adadin danyen mai da aka amince da su. Kamfanin NNPCL ya gaza cika wannan wa’adin da ya kare a ranar 30 ga watan Yunin 2024. Sakamakon haka, an sake bitar kason su zuwa kashi 7.24. Dukkan bangarorin biyu sun ba da rahoton wadannan abubuwan da suka faru.

“Don haka, ba daidai ba ne a yi ikirarin cewa NNPCL ya ciyo bashin dala biliyan 1 domin tallafa wa matatar man Dangote. Kamar duk abokan huldar kasuwanci, NNPCL ya zuba jarin dala biliyan 1 a matatar man domin samun hannun jarin na kashi 7.24 wanda zai amfanar da muradunta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta qara da cewa Kamfanin NNPCPL ya kasance abokin hulda mai kima wajen samun ci gaba, kuma ya zama wajibi ga duk masu ruwa da tsaki su kiyaye gaskiya tare da gabatar da sahihin labari, don jagorantar kafafen yada labarai wajen bayar da sahihin rahoto wanda zai amfanin masu ruwa da tsaki da daukaci al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)
Manyan Labarai

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Next Post
Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.