• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

by Bello Hamza
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Dangote ya musanta labarin da ya karade kakafen yada labarin da ke nuni da cewa kamfanin mai na kasa ya kinkimo bashin dala biliyan guda domin tallafa wa matatan man Dangote.

Dangote ya musanta labarin ne cikin wata sanarwa wanda mai magana da yawun kamfanin, Anthony Chiejina ya fitar a ranar Laraba.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Isa Yankin Macao
  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 

Sanarwar ta ce, “Mun samu tambayoyi da dama daga kafafen yada labarai da sauran masu ruwa da tsaki da ke neman qarin haske kan wani rahoto na baya-bayan nan da aka danganta ga kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), cewa matakin da suka dauka na samun lamuni na dala biliyan 1 daga danyen mai na tallafa wa matatar ta Dangote a lokacin da ya fuskanci kalubalen ba gaskiya ba ne.

 

“Muna so mu fayyace cewa wannan kuskure ne na lamari, domin dala biliyan 1 kusan kashi 5 ne na jarin aka kashe wajen gina matatar Dangote.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

“Shawarar da muka yanke na kulla kawance da NNPCL ya ta’allaka ne kan amincewa da dabarunsu a masana’antar a matsayinsu na masu safarar danyen man fetur mafi girma a Nijeriya a wannan lokacin, su ne kadai suke samar da man fetur a Nijeriya.

“Mun amince kan sayar da hannun jarin kashi 20, kan darajar dala biliyan 2.76. Daga cikin wannan, mun amince da cewa za su biya dala biliyan 1 ne kawai yayin da za a kwato ma’auni na tsawon shekaru 5 ta hanyar cire mana danyen mai da suke kawo mana da kuma ribar da ake samu. Idan da muna cikin kalubalen kudi da ba mu ba su irin wadannan sharuddan biyan kudi masu yawa ba. Kamar yadda a 2021, lokacin da aka sanya hannu kan yarjejeniyar, matatar ta kasance a matakin farko. Bugu da kari, da a ce muna da matsalar kudi, da wannan yarjejeniya ta kasance an biya tsabar kudin nan take.

“Sai dai kuma abin takaicin shi ne, daga baya kamfanin na NNPC ya kasa samar da ganga dubu 300 da aka amince da shi a rana na danyen mai ganin cewa sun sadaukar da mafi yawa daga cikin danyen da suka samu ga masu kudi tare da fatan samun karin hako mai wanda suka kasa cimma ruwa.

“Daga nan kuma muka ba su wa’adin watanni 12 domin su biya cikon kudadensu ganin yadda suka kasa samar da adadin danyen mai da aka amince da su. Kamfanin NNPCL ya gaza cika wannan wa’adin da ya kare a ranar 30 ga watan Yunin 2024. Sakamakon haka, an sake bitar kason su zuwa kashi 7.24. Dukkan bangarorin biyu sun ba da rahoton wadannan abubuwan da suka faru.

“Don haka, ba daidai ba ne a yi ikirarin cewa NNPCL ya ciyo bashin dala biliyan 1 domin tallafa wa matatar man Dangote. Kamar duk abokan huldar kasuwanci, NNPCL ya zuba jarin dala biliyan 1 a matatar man domin samun hannun jarin na kashi 7.24 wanda zai amfanar da muradunta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta qara da cewa Kamfanin NNPCPL ya kasance abokin hulda mai kima wajen samun ci gaba, kuma ya zama wajibi ga duk masu ruwa da tsaki su kiyaye gaskiya tare da gabatar da sahihin labari, don jagorantar kafafen yada labarai wajen bayar da sahihin rahoto wanda zai amfanin masu ruwa da tsaki da daukaci al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiDangoteLabariMatataNNPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Jinping Ya Isa Yankin Macao

Next Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

9 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

16 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

18 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

19 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.