ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Kwanan baya, shugabannin manyan kungiyoyi da cibiyoyin tattalin arziki na duniya sun kawo ziyara ta musamman kasar Sin, inda suka gana da Shugaba Xi Jinping na kasar. Daga cikin tawagar akwai shugabar bankin duniya, Ajay Banga, da darekta-janar ta kungiyar cinikayya ta duniya, Ngozi Okonjo-Iweala. Haka nan, akwai shugaban bankin raya kasashe a karkashin kawancen BRICS, Dilma Rousseff, da kuma manajan darektar asusun ba da lamuni na duniya, Kristalina Georgieva.

 

Wadannan kusoshin na tattalin arziki sun yaba da yadda kasar ta zama madubin dubawa a bangaren tsamar da al’umma daga kangin talauci da sabbin salonta na bunkasa tattalin arziki, kana da irin tallafin da ta dade tana bayarwa ga bunkasa ayyukan kungiyoyin tattalin arzikin duniya.

ADVERTISEMENT
  • Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa
  • Yaƙin Gaza Ya Kusan Zuwa Ƙarshe – Amurka

Hakika, kasar Sin ta jima tana taka rawar gani a janibin raya tattalin arzikin duniya kuma ta sha alwashin ci gaba da zama kashin bayan duniya ta fuskar samar da damammaki da cin moriyar juna a tsakanin kasashen duniya ba tare da nuna bambanci ba.

Sakamakon yadda kasar Sin take samun gawurtar tattalin arziki cikin hanzari fiye da shekaru 40 da ta yi da fara bude kofa, hakan ya sa ta hau turbar samun ci gaba mai inganci, kuma duk da haka har yau ba ta zauna ba, tana kara bullo da gyare-gyare masu zurfi don tabbatar da dorewarsa. Wannan himma ta kasar Sin, ta taimaka wa habakar tattalin arzikin duniya da a kalla kashi 30 cikin dari.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Wani rahoton bankin duniya a shekarar 2022 ya bayyana cewa, daga shekarar 2013 zuwa 2021, kasar Sin take da kimanin kashi 38.6 cikin dari na ci gaban tattalin arzikin duniya. Wannan ya nuna tagomashin da Sin ta kara wa tattalin arzikin duniya ya fi na dukkan hamshakan kasashe mafi bunkasar tattalin arziki na kungiyar G7, inda hakan ya sa kasar ta tsere wa kowa wajen habaka tattalin arzikin duniya.

Ba da fatar baki ne kasar Sin ta zama haka ba, a aikace ne, domin ko a watan Oktoban da ya gabata, bayanan da Hukumar Kididdiga ta Kasar Sin ta fitar sun nuna cewa karfin hada-hadar tattalin arzikin kasar Sin (GDP) a rubu’i na uku na shekarar 2024, ya kai Yuan tiriliyan 94.97, watau kimanin Dala tiriliyan 13.09, wanda yake nuna kasar ta samu karin ci gaba da kashi 4.8 a mizanin shekara-shekara.

Duk da cewa, har yanzu kasar Sin ba ita ce ta farko ba a jerin kasashe mafi karfin tattalin arzikin duniya, ita ce ta biyu, hakan bai sa ta zama marowaciya ba, ta bullo da kawance daban-daban na cin moriyar juna kamar su shawarar “ziri daya da hanya daya” (BRI), dandalin kawancen Sin da Afirka na FOCAC da sauransu. Zuwa yanzu, kasar Sin ta rattaba hannu a yarjejeniyoyin hadin gwiwa a karkashin BRI da fiye da kasashe 150 da kuma manyan kungiyoyin duniya guda 30.

Bugu da kari, wasu bayanai daga ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin sun nuna cewa, zuwa karshen shekarar 2023, kamfanonin kasar Sin sun kafa rassa kimanin 17,000 a kasashen da suka rattaba hannu a shawarar BRI. Wadannan kamfanonin, sun zuba jari kai-tsaye na fiye da Dala biliyan 330, baya ga samar da ayyukan yi a cikin gida a kalla 530,000 daga sassan kawancen tattalin arziki da cinikayya da aka kulla a karkashin shawarar.

Wadannan duka misalai ne da suke nuna yadda tattalin arzikin kasar ke ci gaba da zama bango majinginar duniya kuma kamar yadda Shugaba Xi Jinping na kasar ya alkawarta, kasar za ta ci gaba da bude kofa ga sauran kasashe da tafiya a kan manyan ingantattun dokokin cinikayya na duniya domin cin gajiyar juna. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.