ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

by Bello Hamza
2 years ago
Dangote

Kamfanin Dangote ya musanta labarin da ya karade kakafen yada labarin da ke nuni da cewa kamfanin mai na kasa ya kinkimo bashin dala biliyan guda domin tallafa wa matatan man Dangote.

Dangote ya musanta labarin ne cikin wata sanarwa wanda mai magana da yawun kamfanin, Anthony Chiejina ya fitar a ranar Laraba.

  • Shugaba Xi Jinping Ya Isa Yankin Macao
  • Tinubu Ya Isa Legas Don Gudanar Da Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara 

Sanarwar ta ce, “Mun samu tambayoyi da dama daga kafafen yada labarai da sauran masu ruwa da tsaki da ke neman qarin haske kan wani rahoto na baya-bayan nan da aka danganta ga kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), cewa matakin da suka dauka na samun lamuni na dala biliyan 1 daga danyen mai na tallafa wa matatar ta Dangote a lokacin da ya fuskanci kalubalen ba gaskiya ba ne.

ADVERTISEMENT

 

“Muna so mu fayyace cewa wannan kuskure ne na lamari, domin dala biliyan 1 kusan kashi 5 ne na jarin aka kashe wajen gina matatar Dangote.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Shawarar da muka yanke na kulla kawance da NNPCL ya ta’allaka ne kan amincewa da dabarunsu a masana’antar a matsayinsu na masu safarar danyen man fetur mafi girma a Nijeriya a wannan lokacin, su ne kadai suke samar da man fetur a Nijeriya.

“Mun amince kan sayar da hannun jarin kashi 20, kan darajar dala biliyan 2.76. Daga cikin wannan, mun amince da cewa za su biya dala biliyan 1 ne kawai yayin da za a kwato ma’auni na tsawon shekaru 5 ta hanyar cire mana danyen mai da suke kawo mana da kuma ribar da ake samu. Idan da muna cikin kalubalen kudi da ba mu ba su irin wadannan sharuddan biyan kudi masu yawa ba. Kamar yadda a 2021, lokacin da aka sanya hannu kan yarjejeniyar, matatar ta kasance a matakin farko. Bugu da kari, da a ce muna da matsalar kudi, da wannan yarjejeniya ta kasance an biya tsabar kudin nan take.

“Sai dai kuma abin takaicin shi ne, daga baya kamfanin na NNPC ya kasa samar da ganga dubu 300 da aka amince da shi a rana na danyen mai ganin cewa sun sadaukar da mafi yawa daga cikin danyen da suka samu ga masu kudi tare da fatan samun karin hako mai wanda suka kasa cimma ruwa.

“Daga nan kuma muka ba su wa’adin watanni 12 domin su biya cikon kudadensu ganin yadda suka kasa samar da adadin danyen mai da aka amince da su. Kamfanin NNPCL ya gaza cika wannan wa’adin da ya kare a ranar 30 ga watan Yunin 2024. Sakamakon haka, an sake bitar kason su zuwa kashi 7.24. Dukkan bangarorin biyu sun ba da rahoton wadannan abubuwan da suka faru.

“Don haka, ba daidai ba ne a yi ikirarin cewa NNPCL ya ciyo bashin dala biliyan 1 domin tallafa wa matatar man Dangote. Kamar duk abokan huldar kasuwanci, NNPCL ya zuba jarin dala biliyan 1 a matatar man domin samun hannun jarin na kashi 7.24 wanda zai amfanar da muradunta,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta qara da cewa Kamfanin NNPCPL ya kasance abokin hulda mai kima wajen samun ci gaba, kuma ya zama wajibi ga duk masu ruwa da tsaki su kiyaye gaskiya tare da gabatar da sahihin labari, don jagorantar kafafen yada labarai wajen bayar da sahihin rahoto wanda zai amfanin masu ruwa da tsaki da daukaci al’umma.

Dangote
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.