• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya zama attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka karo na 12 a jere, kamar yadda mujallar Forbes ta ruwaito.

Babban kamfanin Dangote na siminti ne ya ci gaba kasancewa kan gaba wajen samar da siminti a Afirka, kuma Dangote shi ne dan Nijeriya daya tilo a cikin jerin attajirai 200 na farko a duniya wanda darajarsa tai kai dalar Amurka biliyan 14.2, sama da dala biliyan 12.1 da ya samu a bara.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai 1,100
  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciko Wadanda Suke Kashe-Kashe A Filato

A halin yanzu Dangote yana matsayi na 124 a cikin manyan attajiran duniya, kuma shi ne dan Nijeriya daya tilo a cikin jerin manyan attajiran duniya 200 kuma daya daga cikin ‘yan Afirka biyu da ke jerin attajirai; tare da Johann Rupert na Afirka ta Kudu, wanda ya zo na 157 da darajar dukiyar da ta kai dala biliyan 11.1.

Attajirin wanda ya fi kowa kudi a Afirka na jagorantar kamfanin siminti mafi girma a nahiyar Afrika.

Kamfanin siminti na Dangote na samar da tan miliyan 51.6 a kowace shekara a kasashe goma a Afrika, tare da hadakar masana’antu a kasashe bakwai da kuma wasu masana’antu a Kamaru da Ghana da Saliyo.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Dangote ya mallaki kamfanonin gishiri da sukari da ma wasu daban.

Kazalika, attajirin ya mallaki matatar tace mai, wadda ake kyautata zaton za ta zama mafi girma a duniya, wadda tsohon shugaban kasar Nijeriya, shugaba Buhari ya kaddamar kuma ana sa ran za ta sarrafa gangar mai 650,000 don amfanin cikin gida da kuma fitar da shi zuwa kasashen waje.

Mujallar Fortune, wata mujalla ce ta kasuwanci ta kasa da kasa da ke Amurka, ta ayyana Dangote a matsayi na 11 cikin mutum 50 mafi tasiri a duniya a tsakanin ‘yan kasuwa maza da mata.

Mujallar da aka fara buga ta a watan Fabrairun 1930, ta ce attajirim na sauya duniya tare da zaburar da wasu a harkokin kasuwanci da gwamnati wajen ciyar da al’ummarsu gaba.

Dangote ya samu matakin ne bayan da mujallar ta ce attajirin yana amfani da dukiyarsa ta hanyar taimakon jama’a ta gidauniyarsa ta Aliko Dangote.

Mutum 10 maza da mata da mujallar Fortune ta zayyano a matsayin wadanda suka fi kowa tasiri su ne: Bill da Melinda Gates, Jacinda Ardem, Robert Mueller, Pony Ma, Satya Nadella, Greta Thunberg, Margrethe Vestager, Anna Nimiriano, Jose Andres, da Dough Mcmillon da Lisa Woods.

Shi kuwa Dangote an ayyana shi a matsayin daya daga cikin manyan ‘yan kasuwa a fadin duniya wanda ya cancanci a karrama shi ta hanyar basirar kasuwancinsa da kuma ayyukan alheri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArzikiAttajiriDangoteMujallar ForbesMujallar FortuneSiminti
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 5 A Enugu

Next Post

Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

21 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

23 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

24 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

Mark Zuckerberg Ya Fara Daukar Horo Don Yin Dambe Da Elon Musk

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.