Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, tare da hadaka da Gwamnatin Jihar Legas da sauran wasu masu ruwa da tsaki a bangaren tsaro, domin fadar kan jama’a kan mahimmancin tsaftace Tashar Jirgi ta Tin Can Island, da ke a jihar.
Hakan na kunshe ne, a cikin sanarwar da Hukumar ta fitar, inda sanarwar ta bayyana cewa, za ta yi hakan ne, bisa nufin magance duk wasu ayyuka da ke janyo tarnaki a Tashar ta Tin Can Island, musamman domin a samar da walwalar gudanar da ayyuka a Tashar, a cikin sauki.
- Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
- Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
Kazalika, sanarwa ta bayyna cewa, manufar shi ne, domin a dakile ayyukan batagari da sauran masu kaffa shugana a Tashar, ba bisa ka’ida ba, wanda hakan, ke haifar da cunkoson ababen hawa, a Tashar, inda hakan ya zama barazana da lafiyar ma’aikatan da ke a Tashar ta Tin Can Island.
Aikin na tsaftace Tashar Jirgi ta Tin Can Island, ya yi daidai da tsarin kasa da kasa, musamman wajen kara tabbatar da tsaro da wanzar da matakan kungiyar IMO da ke tabbatar da kare zirga-zirgar Jiragen Ruwa a Tekuna, na kasa da kasa, musamman domin a kara tabbatar da samar da kariya da kuma tsaro, adaukacin Tashoshin Jiragen Ruwa, a fadin duniya.
Da yake kaddamar da aikin tsaftace Tashar Jirgen Ruwan ta Tin Can Island, Shugaban Hukumar ta NPA Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, Hukumar ta dauki wannan matakin ne, domin ta tabbatar da samar da kyakyawan yanayi wanda ya yi daidai da na kasa da kasa da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.
“Ya zamar mana wajbi, mu kulla wannan hadakar, musamman domoin mu tabbatar da cewa, mun tsaftace tsarin,” Inji Dantsoho.
Ya kara da cewa, wannan aikin, ba wai kawai za kara habaka samar da kariya da kuma kara ingnata tsaro bane, har da kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara ciyar da tattalin arzikin kasar nan gaba.
A cewar Shugaban, cunkoson da ake samu a Tashar ta Tin Can Island na ci gaba da haifar da jinkiri da rashin gudanar da ayyuka yadda suka kamata da kuma rage gudanar da hada-hadar kasuwanci, yadda ta kamata, wanda kuma hakan, ke janyowa kara habaka tattalin arzikin kasar.
Dantsoho wanda Babban Janar Manaja na sashen kula da tsaro a Hukumar ta NPA Mista Anthony Edosomwan ya wakilce shi a wajen kaddamar da aikin ya bayyana cewa, za a gudanar da aikin ne, zuwa kwana uku, musamman domin a samu nasarar gudanar da aikin.
Shugaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ya wallafa a kafafen yada labarai, kan sanarwar wayar da kan jama’a kan batun mahimmancin, tsaftace Tashar ta Tin Can Island.
“Wannan wani mataki ne, da aka samu goyon bayan masu ruwa da tsaki ciki har da masu yin amfani da Tashar da ‘yan kasuwa da kuma sauran alummar da ke a kusa da yankin”, A cewar Dantsoho.
Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA ba za ta yi kasa a guiwa, wajen kara mayar da hankali da kuma zagewa, domin ta samu cin nasara wajen tabbatar da tsaftace muhalli da kuma samar da kyakyawan yanayi, a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ba.
“Yanayi na samun gurbatacciyar Iska da kutsen da ake yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, abu ne da Hukumar ta NPA, ba za ta rungume hannu ta bari ba, ” Inji Dantsoho.
“Wannan aikin na tsafrace Tashar ba wai kawai na da alfanu ga ayyukan da ake gudanarwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar bane, hatta alumomin da suke daura da Tashoshin, suma zai yi masu alfanu,“ A cewar Shuaban .
Shuaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ta NPA da faro shi a wannan shekarar ta 2025, na daga cikin shiryae-shiryen rage cunkoso da kuma samar da saukin gudanar da ayyuka, Hukumar ta NPA, wanda hakan zai taimaka matuka wajen samar da kyakywar makoma ga Tashoshin Jiragen Ruwa, da ke a daukacin kasar nan.
A cewar Shugaban, wannan hadakar da sauran jami’an tsaro da kuma yin gangamin na wayar da kan alumma, Hukumar na bukatar goyon bayan alumma, dominn ta samu nasarar, aikin da ta sanya a gaba,
“A saboda haka, Mahukuntan Hukumar ta NPA, na bukatar goyon baya da hadin kan jama’a musamman domin a samar da kyakyawan yanin da ya dace a Tashar Jirgin Ruwan,” A cewar Shugaban.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp