• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darasin Da Za Mu Koya Daga Shirin Mata A Yau (II)

by Leadership Hausa
2 years ago
Darasi

LABARAI MASU NASABA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

A irin zamantakewa ta yanzu ba duka iyali ne suke gaisuwa tsakanin miji da mata ba, gara ma dai tsakanin ‘ya’ya da iyayensu ko yayye da kannai.

Wannan ba yana nuna yin gaisuwa tsakanin ma’aurata ba shi da kyau ba ne, tarbiyya ce mai kyau, amma matasan yanzu na ganin kwana daki daya ko gado daya ya dauke wannan bukatar gaisuwar, musamman saboda ganin ana tare kowanne lokaci.

  • Neymar Ya Zarce Pele A Matsayin Wanda Yafi Zurawa Kasar Brazil Kwallaye
  • Tinubu Ya Amince Da Gina Gidaje 1,000 A Jihohin Arewa 7 – Shettima

Wannan na faruwa ne a irin yanayin da zamani ya kawo na canji a halin zamantakewa da ake fuskanta, a kowanne bangaren rayuwa. Dole ne a daidai wannan gaba a rika samun akasi, saboda sauyin da yake shigowa.

Hajiya Aishatu Gidado Idris wata fitacciyar marubuciya kuma mai ba da shawarwari kan zamantakewar iyali ta rubuta cewa, dole ne a kokarin daidaita jiya da yau a zamantakewar rayuwa sai an fuskanci turjiya da kalubale daga al’umma. Wannan haka yake ko a tarihin duniya, duk lokacin da wani sabon tunani ya zo ya ci karo da tsohon tsari, sakamakon ba ya kyau, a wani lokaci ma har asarar rai ake yi da dukiya, saboda nuna bore daga jama’a. Kamar yadda yanzu abubuwan da suka biyo bayan wannan shiri ya daga hankalin masu gabatar da shirin, iyalinsu, mutuncinsu da mu’amalarsu da jama’a, sakamakon yadda aka kasa fahimtar su da mummunar fassarar da ake musu.

A cikin lafazi mai nuna dacin rai, “Hajiya Halima Ben Omar ta ce, shirin Mata A Yau bai taba kawo wata fatawa ko shawara da ta soki koyarwar addinin Musulunci ba, amma muna kokarin ganin an samu canji ga wasu abubuwa da al’ada ce ta kawo su ba addini ba. Sai dai abin mamaki wasu da ko kallon shirin ba su taba yi ba, sun bi duniya suna yada cewa ana fada da koyarwar addini.”

Lallai ne ya kamata wannan ya zama darasi gare mu duka, musamman tashar Arewa 24 da masu shirin Mata A Yau, su sani ana hallare da su, kuma kurar su ta riga da ta yi kuka tuntuni, don haka abu kadan ne za su yi ya zama matsala. Ya kamata su kara hattara da taka-tsantsan, kuma su rika tauna kalamansu suna sanya hikima cikin fadakarwar da suke yi.

Sannan a kokarinsu na ganin sun kawo sauyi da cigaban rayuwar mata su rika fahimtar yanayin al’ummar da suke ciki, tsaurinta kan sha’anin addini da al’ada, da yadda canji ke wuyar samuwa a rayuwar Malam Bahaushe. Haka kuma su rika tuntubar malamai a kai-a kai ana samun fahimtar juna da karin haske kan wasu batutuwan da suke so su bijiro da shi. Na san shirin yana cike da kwararru, dan boko da malamai. Lallai a kara sa ido sosai!

Ya zama wajibi shugabannin tashar Arewa 24 su tashi tsaye wajen ganin sun yi wa kansu gyaran fuska, sun hada kai da malamai da masu fada a ji don kyautata yadda jama’a ke yi musu kallon jakadun yahudawa, masu yaki da addini da gurbata tarbiyya. Su kuma samar da wasu shirye-shirye da jama’a za su gamsu da su cewa, mummunan zaton da ake yi musu ba gaskiya ba ne.

Gare mu masu kallo, yana da kyau mu fahimci cewa kowacce tashar talabijin ko rediyo akwai manufar kafata, kamar yadda na bayyana a farko. Ba zai yiwu kowacce tasha ta zama kamar Sunnah TB ko NTA ba. Akasari tashoshin talabijin na zamani sun fi mayar da hankali ne kan fadakarwa da nishadantarwa. Shi ya sa ko a Arewa 24 bangaren nishadi ke da muhimmanci, domin da shi ne ake daukar hankalin matasa ta yadda manufofin tashar na yaki da tsattsauran ra’ayin addini, cin zarafin mata, da shugabanci nagari, za su samu shiga zukatan matasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

December 29, 2024
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

December 21, 2024
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

May 12, 2024
Next Post
Bukatar Kulawa Ta Musamman Ga Tarbiyar ‘Ya’ya Maza

Bukatar Kulawa Ta Musamman Ga Tarbiyar ‘Ya’ya Maza

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.