ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darasin Da Za Mu Koya Daga Shirin Mata A Yau (II)

by Leadership Hausa
3 years ago
Darasi

LABARAI MASU NASABA

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

A irin zamantakewa ta yanzu ba duka iyali ne suke gaisuwa tsakanin miji da mata ba, gara ma dai tsakanin ‘ya’ya da iyayensu ko yayye da kannai.

Wannan ba yana nuna yin gaisuwa tsakanin ma’aurata ba shi da kyau ba ne, tarbiyya ce mai kyau, amma matasan yanzu na ganin kwana daki daya ko gado daya ya dauke wannan bukatar gaisuwar, musamman saboda ganin ana tare kowanne lokaci.

  • Neymar Ya Zarce Pele A Matsayin Wanda Yafi Zurawa Kasar Brazil Kwallaye
  • Tinubu Ya Amince Da Gina Gidaje 1,000 A Jihohin Arewa 7 – Shettima

Wannan na faruwa ne a irin yanayin da zamani ya kawo na canji a halin zamantakewa da ake fuskanta, a kowanne bangaren rayuwa. Dole ne a daidai wannan gaba a rika samun akasi, saboda sauyin da yake shigowa.

Hajiya Aishatu Gidado Idris wata fitacciyar marubuciya kuma mai ba da shawarwari kan zamantakewar iyali ta rubuta cewa, dole ne a kokarin daidaita jiya da yau a zamantakewar rayuwa sai an fuskanci turjiya da kalubale daga al’umma. Wannan haka yake ko a tarihin duniya, duk lokacin da wani sabon tunani ya zo ya ci karo da tsohon tsari, sakamakon ba ya kyau, a wani lokaci ma har asarar rai ake yi da dukiya, saboda nuna bore daga jama’a. Kamar yadda yanzu abubuwan da suka biyo bayan wannan shiri ya daga hankalin masu gabatar da shirin, iyalinsu, mutuncinsu da mu’amalarsu da jama’a, sakamakon yadda aka kasa fahimtar su da mummunar fassarar da ake musu.

A cikin lafazi mai nuna dacin rai, “Hajiya Halima Ben Omar ta ce, shirin Mata A Yau bai taba kawo wata fatawa ko shawara da ta soki koyarwar addinin Musulunci ba, amma muna kokarin ganin an samu canji ga wasu abubuwa da al’ada ce ta kawo su ba addini ba. Sai dai abin mamaki wasu da ko kallon shirin ba su taba yi ba, sun bi duniya suna yada cewa ana fada da koyarwar addini.”

Lallai ne ya kamata wannan ya zama darasi gare mu duka, musamman tashar Arewa 24 da masu shirin Mata A Yau, su sani ana hallare da su, kuma kurar su ta riga da ta yi kuka tuntuni, don haka abu kadan ne za su yi ya zama matsala. Ya kamata su kara hattara da taka-tsantsan, kuma su rika tauna kalamansu suna sanya hikima cikin fadakarwar da suke yi.

Sannan a kokarinsu na ganin sun kawo sauyi da cigaban rayuwar mata su rika fahimtar yanayin al’ummar da suke ciki, tsaurinta kan sha’anin addini da al’ada, da yadda canji ke wuyar samuwa a rayuwar Malam Bahaushe. Haka kuma su rika tuntubar malamai a kai-a kai ana samun fahimtar juna da karin haske kan wasu batutuwan da suke so su bijiro da shi. Na san shirin yana cike da kwararru, dan boko da malamai. Lallai a kara sa ido sosai!

Ya zama wajibi shugabannin tashar Arewa 24 su tashi tsaye wajen ganin sun yi wa kansu gyaran fuska, sun hada kai da malamai da masu fada a ji don kyautata yadda jama’a ke yi musu kallon jakadun yahudawa, masu yaki da addini da gurbata tarbiyya. Su kuma samar da wasu shirye-shirye da jama’a za su gamsu da su cewa, mummunan zaton da ake yi musu ba gaskiya ba ne.

Gare mu masu kallo, yana da kyau mu fahimci cewa kowacce tashar talabijin ko rediyo akwai manufar kafata, kamar yadda na bayyana a farko. Ba zai yiwu kowacce tasha ta zama kamar Sunnah TB ko NTA ba. Akasari tashoshin talabijin na zamani sun fi mayar da hankali ne kan fadakarwa da nishadantarwa. Shi ya sa ko a Arewa 24 bangaren nishadi ke da muhimmanci, domin da shi ne ake daukar hankalin matasa ta yadda manufofin tashar na yaki da tsattsauran ra’ayin addini, cin zarafin mata, da shugabanci nagari, za su samu shiga zukatan matasa.

Darasi
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Marurun Zuciya

Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

May 23, 2026
marayu
Marurun Zuciya

Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

May 17, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Marurun Zuciya

2027: Bukatar Zaben Shugabanni Na Gari

May 10, 2026
Next Post
Bukatar Kulawa Ta Musamman Ga Tarbiyar ‘Ya’ya Maza

Bukatar Kulawa Ta Musamman Ga Tarbiyar ‘Ya’ya Maza

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.