• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

by Ibrahim Muhammad
1 year ago
in Labarai
0
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matakin Shugaban kasa, Bola Tinubu na kirkiro ma’aikatar bunkasa harkokin kiwo na ci gaba da janyo zafafan muhawara a tsakanin masu ruwa da tsaki.

Ko da yake, wani Lauya mai suna Madubuachi Idam, na kallon yunkurin na Tinubu a matsayin asara, domin akwai wasu ma’aikatun da ke da manufa irin aikin da wannan za ta yi, yayin da kuma kungiyar ci gaban matasan arewa (AYCF) da Afenifere da kuma Ohanaeze Ndigbo da suke da amannar wannan yunkurin abu ne mai kyau da zai iya kawo karshen matsalolin da ake samu tsakanin manoma da makiyaya.

  • Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar
  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

Tinubu ya kirkiri ma’aikatar ne da nufin kawo karshen rigingimun da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya da kuma ganin an inganta harkokin da suka shafi kiwo a fadin kasar nan.

Tun da farko dai, Tinubu ya kafa kwamiti bayan da ya amshi rahoton yadda za a bunkasa harkokin kiwon a kasar nan, wanda Abdullahi Ganduje ya jagoranta, kuma kwamitin ya gabatar da rahotonsa watanni goma da suka gabata da ya bayar da shawarar samar da ma’aikatar.

Sama da shekaru dai an jima ana samun rigingimu a tsakanin manoma da makiyaya wanda hakan ya janyo asarar rayuka da dukiyoyin da ba za su misaltu ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Jihohi kamar su Filato, Benuwai, Kaduna, Inugu, Imo, Delta, Oyo da wasu jihohin na daga cikin wuraren da aka fi samun wadannan matsalolin.

Sai dai Tinubu ya ce, ta hanyar samar da sabuwar ma’aikatar za a samu nasarar dakile wannan matsalar. Ya nuna cewa, shiga gonakai a yi barna da kuma toshe wa dabbobi hanyoyin kiwo duk za su samu sauki kuma za a samu rage asarar abinci da rage kaIfin matsaloli ta wannan ma’aikatar.

Sai dai Lauya Madubuachi Idam, ya soki lamarin da cewa an kirkiro ma’aikatar ne domin asarar dukiya a daidai lokacin da jama’an kasa ke kukan talauci da fatara.

Ya ce a maimakon hakan, kamatuwa ya yi a maida hankali kan ma’aikatar gona wanda za ta iya shawo kan lamuran da suka shafi kiwo ba wai sake kirkiro wata ma’aikata don bata kudin kasa ba.

Shi kuma a bangarensa, shugaban kungiyar ci gaban matasan arewa AYCF, Yerima Shettima, ya ce, kirkiro wannan ma’aikatar da Tinubu ya yi tabbas abun a jinjina masa ne kuma yanzu na da abun da zai iya bugan kirji ya nuna wa ‘yan Nijeriya cewa ya yi.

Shettima, ya yi fatan cewa ma’aikatar za ta samu nasarar kawo karshen rigingimun da ake samu a tsakanin manoma da makiyaya, duk da ya misalta matakin a matsayin abun murna matuka.

Ya ce, “Mun yi murna sosai da muka ji labarin an samar da ma’aikatar kula da lamuran kiwo wannan na nuni da cewa gwamnatin nan na da abun da za ta nuna wa ‘yan Nijeriya cewa ta yi wajen ganin ta kawo karshen rikicin manoma da makiyaya.”

Ita ma kungiyar Fulanin ta MACBAN ta bakin daraktan yada labaranta reshen Jihar Kaduna, Ibrahim Bayero Zango, ya ce, tabbas ma’aikatar za ta share hawayen matsalolin da suke akwai kuma za ta kawo mafita ga rikicin manoma da makiyaya.

Zango ya sanya kafa ya shure ikirarin da ke cewa kirkirar ma’aikatar bata kudi ne kawai. Ya ce, ko da wasa ba asarar kudi za a yi ba, illa daura kasar zuwa turbar ci gaba.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan lamarin, darakta janar na kungiyar Ohanaeze, Okechukwu Isiguzoro, ya ce, ma’aikatar za ta shiga tsakanin rikicin manoma da makiyaya da kuma kawo mafita ta karshe, don haka ne suka jinjina wa samar da ma’aikatar.

Haka su ma kungiyar ci gaban al’ummar Yarbawa, Afenifere, ta ce dukkanin wani yunkurin da zai kawo karshen kai hare-haren tsakanin manoma da makiyaya abun yabawa ne kuma tabbas suna goyon bayan wannan yunkurin.

Kakakin kungiyar, Kwamarat Jare Ajayi, ya ce, ba su kallon matakin na Tinubu a kokarin fifita wani yanki ko wata kabila, illa wani mataki da zai kawo karshen matsalolin manoma da makiyaya. Ya nuna cewa ana samun matsalar rikicin manoma da makiyaya a kowani sassa na kasar nan, don haka ba wata kabila ko zallar yanki ne za su mori wannan ma’aikatar ba, illa dukkanin kasar ce za ta mora.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JegaLivestockSaniyaShanuTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Next Post

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

4 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

5 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

6 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

8 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

10 hours ago
Next Post
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.