• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dauda Lawal: Abubuwa 12 Game Da Dan Takarar PDP A Zamfara

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Dauda Lawal: Abubuwa 12 Game Da Dan Takarar PDP A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Laraba 25 ga watan Mayu 2022 ne, Dakta Dauda Lawal ya samu nasarar zama dan takarar Gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara a zaben da za a gabatar a 2023.

Babban abu mafi muhimmanci a siyasa shi ne samar da shugabanin masu nagarta da aminci.

  • Yanzu-yanzun: Tinubu Ya Kai Wa Buhari Ziyara A Fadarsa Abuja

Haka kuma babban makasudin gudanar da zaben fidda gwani a jam’iyyu shi ne samar da damar zabar wadanda al’umma suke so, suka kuma tabbatar da za su yi musu aiki yadda ya kamata, kuma wanda al’umma ke matukar kauna. A kan haka dole a jinjina wa shugabanni da ‘yan jam’iyyar PDP reshen Jihar Zamfara bisa yadda suka gudanar zaben fidda gwani a cikin nasara, inda suka zabo Dakta Dauda Lawal a mastayin wanda zai fafata da sauran jam’iyyu don neman kujerar gwamnan Jihar Zamfara.

Mulkin Jiha kamar Zamfara mai cike da kalubale daban-daban kuma a irin wannan lokaci na mulki dimokradiyya abu ne mai matukar wahala, amma yayin da aka samu kwarewa da sanin makaman aiki abin zai zama da matukar sauki.

A karon farko a tarihin Jihar Zamfara za a tafka zaben Gwamna da kwareraren dan takara Dakta Dauda Lawal. Ga jerin wasu abubuwa masu muhimmanci guda 12 da ya kamata ka sani dangene da Dakta Dauda Lawal:
1. An haife shi a ranar 2 ga watan Satumbar 1965 a garin Gusau, babban birnin Jihar Zamfara. Ya yi digirinsa na farko a fannin Kimiyyar Siyasa (Political Science) a Jami’ar Ahmadu Bello Zariya dake Jihar Kaduna. A bisa yaba wa a kan harkokinsa na tallafa wa al’umma ne ya sa Jami’ar Usman Danfodio Sakkwato ta karrama shi da digirn-digirgir, Haka kuma Jami’ar IHERIS ta kasar Togo ita ma ta karrama shi da digirin-digirgir, yana kuma daga cikin wadanda aka karramar a babban taron ‘African Achiebers Award 2021’ da aka yi a Kensington Palace da ke Landan a kasar Birtaniya.
2. Bayan dawowarsa gida Nijeriya a shekarar 2003, Dauda Lawal ya shiga aikin Banki da ayyukan tallafa wa al’umma, ya kuma samu halartar kwasa-kwasai da dama a ciki da wajen Nijeriya; ciki har da Babbar Makarantar Kasuwanci ta ‘Harbard Business School’ da ke Amurka, Makaratar Kasuwanci ta ‘London Business School’, da ‘Wharton Business School’ da ke Pennsylbania, da ‘Odford Unibersity Business School, International Faculty of Finance, da ke Landan, da ‘Fitch Training’ da ke Landan da New York, haka kuma ya halarci ‘The Asian Banker, Accenture’ da ‘Lagos Business School’, da kuma ‘Euromoney, Ernst and Young’ a inda ya sami cikakkiyar kwarewa a fanin sarrafawa da mu’amala da kudi a mahangar masanan bangaren duniya.
3. Dakta Dauda Lawal ya yi aiki tukuru don ya cimma burinsa. Ya yi aiki a kwamitin gudanarwa First Bank a shekarar 2012 daga nan ne aka dauke shi aiki a matsayin Babban Darakta mai kula yankin Arewa. Ya kuma zama mataimakin shugaba mai kuma da bangaren kamfanoni masu zaman kansu na yankin arewa, ya kuma rike manyan mukamai a bankin ciki har da Babban Manaja mai kula da harkokin kasuwanci (BDM) a reshen bankin na unguwar Maitama dake Abuja, inda ya samu nasarar bunkasa harkokin bankin a babban birnin tarayya da kewaye.
4. Yana da sanin makaman aiki na fiye da shekara 26 wanda ya hada da kwarewa a bangaren kasuwanci da bangaren kamfanoni masu zaman kansu. Tsayuwa da kwarewarsa ta kashi ga matsayinsa na yanzu na Babban Darakta. Sau biyu yana karbar lambar karramawa a matsayin gwarzon shugaban bankin ‘First Bank’, a shekarar 2006 ya zama “Gwarzon Manaja Mai Bunkasa Kasuwanci”, a shekarar 2009 kuma ya samu kyautar “Gwarzon Ma’aikaci Mai Kawo Cigaba”.
5. Dakta Dauda Lawal mamba ne a kungiyoyin masana da dama da suka hada da ‘Institute of Credit Administration of Nigeria’, ‘Fellow of the Cibilian Institute of Democratic Administration of Ghana’, ‘Member of the Institute of Directors, Nigeria’, African Business Roundtable’ da kuma ‘Institute of Corporate Administration, Nigeria’.
6. Dakta Dauda Lawal ya yi fiye da shekara 25 yana aiki a bangaren Bankuna, ya fara tun daga kasa har zuwa kololuwar mataki a aikin bankin. A shekarar 2018 ya ajiye aiki a matsayin Babban Darakta a ‘First Bank’, banki mafi dadewa a Nijeriya. Lawal na kashe kudadensa ne don tallafa wa al’umma musamman a bunkasa ilimi.
7. Ana iya ganin irin tallafin da Lawal yake yi musamman a Jami’ar Gwamnatin Tarayya ta Gusau inda ya gina hanya mai tsawon kilomita uku da rabi, da dakin maigadi a babar kofar shiga jami’ar. Ya kuma gina dakin dalibai mata guda 350 na dalibai maza guda 250 a makarantar Jinya da Unguwar Zoma ta Gusau, ya kuma biya kudaden da aka tantance kwasakwasan da ake karantarwa a makarantar. Ya kuma samu nasarar gina dakin karatu guda hudu a makarantar Kiwon lafiya ta Tsafe. Ya gina masallatai da islamiyyu da dama ya kuma gina makarbar na zamani a garin Gusau.
8. Tallafin da Lawal yake bayarwa ya wuce jiharsa ta Zamfara, ya gina azuzuwa a makarantar ‘Yan sanda ta Kaduna; ya kuma gina Masallaci da islamiyya dukkaninsu a Kaduna. Ya gyara azuzuwa da dakin daukar darasin kwamfuta a Makarantar Sakandire ta Gwamnati da ke Kachia a Jihar Kaduna. Haka kuma shi ne ya gida babban masallacin Juma’a na ITN a Zariya, ya kuma gyara shaharariiyar masallacin nan na tashar jirgin kasa da ke Kaduna.
9. A Jami’an Ahmadu Bello Zariya, inda ya yi karatun jami’arsa, ya gina dakin karatu mai hawa uku hade da ofishoshin ma’aikata, ya kuma samarwa tsangayar kimiyyar siyasa mota bas don zirga zirga. Ya kuma gina rukunin azuzuwa a tsangayar koyar da kiwon lafiya ta Jami’ar Usman Danfodio da ke Sakkwato.
10. Haka kuma Dauda Lawal ya kai tallafi kauyen Guga ta Jihar Katsina, mahaifar mahaifiyarsa inda a nan ne ya yi makarantar firamarensa, ya gina asibiti na zamani, ya gyara makarantun garin, ya samar da cibiyar koyar da kwanfuta, ya kuma samar musu da rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana (solar).
11. Don rage zaman kashe wando da samar da ayyukan yi ga al’umma Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samar da ma’aikatar yin blok na ‘Zam blocks’, gidan blok mafi girma a Jihar Zamfara. Ya kuma kafa kamfanin shinkafa ta ‘Zam rice mills’ da kamfanin ruwa na ‘Azuma water’ da kamfanin takin zamani na ‘Zam agrochemical’ (Kamfanin taki mafi girma a arewacin Nijeriya).
12. a ranar 30 ga watan Janairu 2022, dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya dauki nauyin ‘yan asali Jihar Zamfara 120 zuwa Jami’ar IHERIS ta kasar Togo don don suyi karatu a matakin digirin farko dana biyu. Tallafin karatun ga dalibai 120 an yi ne ta hannun gidauniyar Dr. Dauda Lawal, za kuma su yi karatu ne a bangarorin Ilimin Kwamfuta, Kimiyya da Fasaha, Ilimin tafiyar da harkokin gwamnati, Harkokin kasashe waje, Ilimin sarrafa kwanfuta da sauransu.
Tabbas Jihar Zamfara ta yi dace da samun haziki kuma kwararre irin Dauda Lawal, muna fatan al’umma za su bashi goyon baya don kai Jihar Zamfara tudun-mun-tsira.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

Next Post

Goron Jumu’a

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

3 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

3 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

4 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

5 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.