• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowar Ta’asar Boko Haram: An Kashe Maciji Ba A Sare Kan Ba – Mazauna Gabas

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
boko haram
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jama’a sun fara bayyana shakku dangane da yadda a ‘yan kwanakin nan ake fuskantar barazanar dawowar hare-haren mayakan kungiyar Boko Haram a jihohin Borno da Yobe, a daidai lokacin da ake tsammanin an raka bako; ashe yana labe a bayan gari.

Hakan ya biyo bayan wasu munanan hare-haren da mayakan ke ci gaba da aiwatar wa a wasu sassan jihohin biyu, wadanda suka dade suna fada da rikicin wanda ya jawo asarar dimbin rayukan al’umma tare da barnata dukiya ta biliyoyin naira; baya ga raunata dubban jama’a.

  • Zulum Ya Daukaka Darajar Kwalejin Larabci Zuwa Babbar Cibiyar Yaki Da Akidun Boko Haram
  • ISWAP Ta Hallaka Kwamandan Boko Haram A Sambisa

Cikin kasa ga wata daya, mayakan sun aiwatar da munanan hare-haren da suka jawo salwantar rayuka sama da 50, wanda a makon da ya gabata, mayakan sun kashe kimanin mutum 40 a kauyen Nguro-kayya dake karamar hukumar Gaidam a jihar Yobe, baya ga halaka wani jami’in hukumar hana fasa kauri ta Nijeriya a garin na Gaidam.

Yayin da a cikin wannan makon, mayakan na Boko Haram sun halaka manoman shinkafa 13, a cikin wani sabon harin d suka kai a kauyukan Karkut da Koshebe dake cikin karamar hukumar Mafa a jihar Borno.

LEADERSHIP Hausa ta zanta da wani magidanci daga garin Gaidam (bai aminta a bayyana sunan sa ba) a jihar Yobe, ya ce: “Zancen a ce babu Boko Haram bai taso ba, saboda kusan kana fita daga garin Gaidam kadan; ta bangaren gabas da Arewaci, za ka ci karo da yan Boko Haram, wanda tun a wancan lokacin su suke karbar haraji a hannun mazauna kauyuka.”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Gaskiyar magana ita ce, har yanzu akwai sauran rina a kaba, saboda har yanzu yaran nan (Boko Haram) suna nan a kauyuka, ba sa jin tsoro ko shakkar wani mutum. Suna nan a cikin tsaunuka da dazuka tare da wasu kauyuka.”

“Kuma abin da ya sa ba a jin diriyarsu a lokacin damina shi ne gittawar ruwan Kogin Kumadugu, amma da zaran ya yanke za kana ganin su. Musamman tun daga gabashin Gaidam har zuwa Tafkin Chadi, wanda ana iya cewa sun mayar da yankin tamkar daularsu. Babu abin da mutum zai yi har sai da izinin su tare da biyan haraji.” Ya bayyana.

Shi ma wani bawan Allah da wakilinmu ya tattauna da shi ta wayar tafi da gidanka (bai yarda na bayyana sunan shi ba, saboda yanayin tsaro) a Yadin-Buni dake jihar Yobe, ya bayyana cewa, “ba zan ce ba a gama da Boko Haram ba, to amma gaskiyar magana shi ne an kashe maciji ba a sare kansa ba. Saboda har yanzu akwai yankunan da ba ma shiga a nan.”

“Idan ba ka manta ba, a kwanan baya ma sun yi wa wasu matasanmu sama da 10 kwanton-bauna, inda suka halaka su har lahira. Sannan har yanzun nan da nake magana da kai, kowane lokaci a cikin fargaba al’ummar kauyukanmu suke; saboda kowane lokaci zaman dar-dar ake.” In ji shi.

Jama’a da dama a wadannan jihohin suna ci gaba da bayyana ra’ayoyi daban-daban dangane da sabbin hare-haren tare da bayyana cewa ya kamata gwamnati ta sake nazarin matakan da ta bi wajen karbar tuban wasu daga cikin mayakan Boko Haram da ta yi a baya, inda ra’ayoyin ke nuni da cewa sai da dan gari a kan ci gari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaBornoISWAP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

Next Post

Cire Kashi 40 Na Kudin Shigar Jami’o’i Zai Kassara Su – ASUU

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
ASUU

Cire Kashi 40 Na Kudin Shigar Jami’o’i Zai Kassara Su - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.