ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowar Ta’asar Boko Haram: An Kashe Maciji Ba A Sare Kan Ba – Mazauna Gabas

by Muhammad Maitela
3 years ago
boko haram

Jama’a sun fara bayyana shakku dangane da yadda a ‘yan kwanakin nan ake fuskantar barazanar dawowar hare-haren mayakan kungiyar Boko Haram a jihohin Borno da Yobe, a daidai lokacin da ake tsammanin an raka bako; ashe yana labe a bayan gari.

Hakan ya biyo bayan wasu munanan hare-haren da mayakan ke ci gaba da aiwatar wa a wasu sassan jihohin biyu, wadanda suka dade suna fada da rikicin wanda ya jawo asarar dimbin rayukan al’umma tare da barnata dukiya ta biliyoyin naira; baya ga raunata dubban jama’a.

  • Zulum Ya Daukaka Darajar Kwalejin Larabci Zuwa Babbar Cibiyar Yaki Da Akidun Boko Haram
  • ISWAP Ta Hallaka Kwamandan Boko Haram A Sambisa

Cikin kasa ga wata daya, mayakan sun aiwatar da munanan hare-haren da suka jawo salwantar rayuka sama da 50, wanda a makon da ya gabata, mayakan sun kashe kimanin mutum 40 a kauyen Nguro-kayya dake karamar hukumar Gaidam a jihar Yobe, baya ga halaka wani jami’in hukumar hana fasa kauri ta Nijeriya a garin na Gaidam.

ADVERTISEMENT

Yayin da a cikin wannan makon, mayakan na Boko Haram sun halaka manoman shinkafa 13, a cikin wani sabon harin d suka kai a kauyukan Karkut da Koshebe dake cikin karamar hukumar Mafa a jihar Borno.

LEADERSHIP Hausa ta zanta da wani magidanci daga garin Gaidam (bai aminta a bayyana sunan sa ba) a jihar Yobe, ya ce: “Zancen a ce babu Boko Haram bai taso ba, saboda kusan kana fita daga garin Gaidam kadan; ta bangaren gabas da Arewaci, za ka ci karo da yan Boko Haram, wanda tun a wancan lokacin su suke karbar haraji a hannun mazauna kauyuka.”

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“Gaskiyar magana ita ce, har yanzu akwai sauran rina a kaba, saboda har yanzu yaran nan (Boko Haram) suna nan a kauyuka, ba sa jin tsoro ko shakkar wani mutum. Suna nan a cikin tsaunuka da dazuka tare da wasu kauyuka.”

“Kuma abin da ya sa ba a jin diriyarsu a lokacin damina shi ne gittawar ruwan Kogin Kumadugu, amma da zaran ya yanke za kana ganin su. Musamman tun daga gabashin Gaidam har zuwa Tafkin Chadi, wanda ana iya cewa sun mayar da yankin tamkar daularsu. Babu abin da mutum zai yi har sai da izinin su tare da biyan haraji.” Ya bayyana.

Shi ma wani bawan Allah da wakilinmu ya tattauna da shi ta wayar tafi da gidanka (bai yarda na bayyana sunan shi ba, saboda yanayin tsaro) a Yadin-Buni dake jihar Yobe, ya bayyana cewa, “ba zan ce ba a gama da Boko Haram ba, to amma gaskiyar magana shi ne an kashe maciji ba a sare kansa ba. Saboda har yanzu akwai yankunan da ba ma shiga a nan.”

“Idan ba ka manta ba, a kwanan baya ma sun yi wa wasu matasanmu sama da 10 kwanton-bauna, inda suka halaka su har lahira. Sannan har yanzun nan da nake magana da kai, kowane lokaci a cikin fargaba al’ummar kauyukanmu suke; saboda kowane lokaci zaman dar-dar ake.” In ji shi.

Jama’a da dama a wadannan jihohin suna ci gaba da bayyana ra’ayoyi daban-daban dangane da sabbin hare-haren tare da bayyana cewa ya kamata gwamnati ta sake nazarin matakan da ta bi wajen karbar tuban wasu daga cikin mayakan Boko Haram da ta yi a baya, inda ra’ayoyin ke nuni da cewa sai da dan gari a kan ci gari.

boko haram
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
ASUU

Cire Kashi 40 Na Kudin Shigar Jami’o’i Zai Kassara Su - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.