• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimbin Falalar Raya Dararen Goman Karshe

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Dimbin Falalar Raya Dararen Goman Karshe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A uzu billahi minas shaidanir rajim. Bismillahir rahmanir rahim. Wa sallallahu alan Nabiyyil karim. Assalamu alaikum warahmtullahi Ta’ala wa barkatuh.

Masu karatu barkan mu da sake haduwa a wannan makon domin ci gaba da darasinmu kan abin da ya shafi Azumin Ramadan.

  • Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 
  • Da Dumi-dumi: APC Ta Dakatar Da Dan Majalisar Wakilai Shehu Koko 

Mun shiga goman karshe na watan Azumin bana, wanda ake fatan ‘yan’uwa Musulmi za a kara dagewa domin neman falalar Allah a ciki.

Hadisi ya tabbata daga Uwar Muminai Aisha (RA) cewa “Manzon Allah (SAW) ya kasance idan Goman karshe na watan Ramadan ta shiga, yakan raya dararanta gaba daya (ma’ana ba ya barci), sai ya tayar da iyalansa (su tashi su yi ibada) kuma ya daura mayafinsa (ma’ana kara kokari).

Har ila yau, a cikin dararen ne ake samun babbar garabasar nan ta daren Lailatul Kadri.

Labarai Masu Nasaba

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

Falalar Daren Lailatul Kadri

Lailatul Kadri dare ne mai girma wanda a cikinsa ne Allah (SWT) ya saukar da Alkur’ani. Annabi (SAW) ya yi bayanin cewa ana samun daren a cikin goman karshen Ramadan cikin mara (kwanukan da za a kirga a samu ragowar daya a ciki watau 21, 23, 25, 27, 29).

Abdullah bin Abbas (RA) ya ce “Allah ya saukar da Alkur’ani gaba daya daga Lauhil Mahfuz zuwa sama ta daya a cikin daren Lailatul Kadri.” Daga nan ne Mala’ika Jibrilu ya rika sauko da shi aya-aya ko sura-sura kamar dai yadda Allah ya umurce shi ya yi.

A wani kaulin ana cewa Mala’ika Israfilu ne ya dauko Alkur’anin daga Allah zuwa Lauhil Mahfuz, su kuma Mala’ikun da ake kira da Kiramun Barara suka dauko shi zuwa sama ta daya, daga nan shi kuma Mala’ika Jibrilu ya rika sauko da Wahayinsa ga Annabi (SAW).

Allah Ta’ala ya albarkaci mu al’ummar Annabi Muhammad (SAW) fiye da sauran al’ummomin da suka gabata kamar yadda rayuwar Maigidan namu (SAW) ta fifici ta sauran Annabawa.

A kan haka ne Allah ya ba mu Daren Lailatul Kadri wanda ya fi watanni 1000, kimanin sama da shekara 83. A ko wace shekara, duk Musulmi idan ya yi Ramadan tare da kudurcewa a ransa na samun daren (walau ya gani ko bai gani ba), Allah zai rubuta masa ladan daren. Wannan yana nuna cewa a duk Ramadan, muna da shekara 83 da ‘yan kai kari a kan shekarunmu. Misali, idan mutum ya riski Ramadan sau 40, yana da karin shekaru na ibada dare da rana masu albarka zalla 83 sau 40 wanda zai bashi jimillar shekara dubu uku da dari uku da ashirin (3320). Wannan falala ce ta Allah ga mu al’ummar Annabi (SAW), alhamdulillah.

Wakazalika, saboda falalar da dararan na goman karshe suka kunsa ne ‘yan uwa Musulmi suka zabi yin ibadar Ittikafi a ciki.

Yadda A Ke Ittikafi

Ittikafi (zaman ibada a cikin masallaci dare da rana) Sunnar Manzon Allah (SAW) ce mai girma. Ma’anar ittikafi ita ce koyi da Mala’ikun Allah. Su Mala’iku ba sa ci; ba sa sha, ba sa barci da dare. Haka nan kai ma mai yin ittikafi ba ka ci; ba ka sha da rana, da dare kuma ba ka barci sai ibada. Amma da rana mutum zai iya yin barci.

Ittikafi ba waje ne na surutai da hira da sauran abubuwa na sharholiya ba.

Malamai sun yi bayanin cewa ba a yin ittikafi sai a Masallacin Jumma’a saboda ba a son fita idan an shiga matukar ba a kammala ba; sai idan akwai lalura. Amma wasu Malaman sun ce za a iya yi ko a Masallacin da ba na Jumma’a ba.

Idan mutum ba shi da mai kawo ma sa abinci zai iya fita ya sayo da kansa amma da zaran ya ci kar ya zauna zaman hira. Idan akwai mai kawo ma sa abincin sai kuma ya fita, to ittikafinsa ya baci sai ya sake shiga sabo. Fita daga Masallaci koda da taku kadan ne ba tare da wata lalura ba tana bata ittikafi.

Ana so mai ittikafi ya dukufa da yawan sallolin nafila, da karatun Alkur’ani da Zikiri. Za a iya yin magana a kan ilmi kamar su Tafsiri, Hadisi, Fikhu, Tarihin Annabawa da Waliyyai da sauran Salihan Bayi. Amma ban da irin yadda wasu ke wa’azi na zage-zage a wannan zamanin.

Mai ittikafi zai iya raka wani da ya ziyarce shi amma ba da nisa ba. Mai yi zai rika tsaftace kansa kamar su wanka da wanki, da yanka farce, da aski, da sauran su saboda shi ba kamar wanda ya daura harami ba ne.

Tambihi

‘Yan uwa Musulmi, mu yi kokari mu ci gajiyar dimbin rahamar da Allah (SWT) ya tanadar mana a wannan wata mai albarka. Saboda akwai tsoratarwa daga Annabi (SAW) kan wanda ya kasa aikata wani abu da zai samu rahamar da Allah Ta’ala ya tanada a watan.

Ya zo a cikin wani Hadisin Jibrilu cewa wata rana Annabi (SAW) zai hau mumbari sai aka ji lokacin da ya taka matakala ta farko yana cewa “amin”, da ya taka matakala ta biyu ya sake cewa “amin, aka kara ji a matakala ta uku ya ce “amin.

Da aka tambaye shi a kan amin din da ya yi ta fada sai ya ce “Jibrilu ya fada mun cewa duk wanda ya riski iyayensa biyu amma ya ki yi masu alherin da zai sa su ji dadi su sanya masa albarka ya shiga aljanna; to idan Allah ya sa shi a wuta ya danna shi a can ciki! Na ce amin. Jibrilu ya kara ce mun wanda ya riski Ramadan bai yi abin da Allah zai gafarta masa ba; idan Allah ya sa shi a wuta ya danna shi a can ciki sai na ce amin….”

Don haka idan mutum bai samu damar yin wani abu da zai samu rahama da gafarar Allah ba, to ya yi kokari a wannan goman ta karshe ya yi don ya samu shiga cikin bayin da Allah zai ‘yanta daga wuta da falalarsa musamman ita dama goma ce ta ‘yantarwa daga wuta zuwa aljanna.

A cikin aljannar ma akwai martabobi da mutum zai nema saboda ita hawa-hawa ce. Haka nan Yardar Allah ta fi aljanna baki dayanta dadi, Ganin Allah kuma ya fi su duka kamar yadda ya zo a cikin karatuttuka.

Saboda haka ‘yan uwa mu dage, Allah ya taimaka mana da falalarsa da rahamarsa ya ba mu ikon aikata abin da zai kai mu wurin da aka fi neman mu isa.

Za mu dakata a nan sai Allah ya kai mu mako mai zuwa. Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadiy wa ala alihi hakka kadirihi wa mikdarihil aziym.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalalaGoman KarsheMusulunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Karuwar Hare-haren Ta’addanci Bayan Zaben 2023

Next Post

Fyade: Abubuwan Da Ke Hadasawa, Illoli Da Yadda Za A Magance

Related

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

2 weeks ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

3 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

1 month ago
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Dausayin Musulunci

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

2 months ago
Next Post
Fyade: Abubuwan Da Ke Hadasawa, Illoli Da Yadda Za A Magance

Fyade: Abubuwan Da Ke Hadasawa, Illoli Da Yadda Za A Magance

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.