• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Dole A Hada Karfi Wajen Dakile Bazuwar Makamai A Afirka –Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce Nijeriya ta kwato yankuna daga hannun ‘yan ta’adda ta hanyar zuba jarin sama da Dala biliyan 1 (N445bn na kasuwanci ko kuma Naira biliyan 740 a kasuwar bayan fage) domin sayo makamai daga Amurka da sauran kasashe kawaye domin ci gaba da yaki da ayyukan da ta’addanci tun daga 2015.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron zaman lafiyar Afirka na 2023, da aka gudanar a Nouakchott, Jamhuriyar Musulunci ta Mauritania.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Shugaba Buhari wanda taron zaman lafiya na Abu Dhabi ya karrama shi da lambar yabo ta Gwarzon Wanzar Da Zaman Lafiya a Afirka “Award for Strengthening Peace in Africa”, ya ce akwai bukatar a samar da dabi’u da bin ka’idoji na hakuri da zaman lafiya a cibiyoyin ilimi, musamman a tsakanin matasa.

Ya bukaci shugabanni da su ba da fifiko kan ci gaban matasa, tare da taka tsantsan da ra’ayoyin da za a iya aiwatar da su wajen inganta sana’o’i, tare da magance zaman kashe wando.

Shugaban ya ce zaman banza ga matasa da rashin sanya hannu wajen tattaunawa kan batutuwan da suka shafi rayuwarsu da kuma makomarsu na nuni da alhakin da ke tattare da nahiyar musamman a bangaren tsattsaurara ra’ayi ga masu tsattsauran ra’ayin.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Shugaba Buhari, a wata sanarwa da mai magana da yawunsa Femi Adesina ya fitar, ya ce dole ne a hada karfi da karfe wajen dakile yaduwar kananan makamai da kuma hana yaduwar manyan makamai a nahiyar Afirka.

Shugaban ya yi kira kan muhimman batutuwan taron kolin kungiyar Tarayyar Afirka na gaba da su yi nazari mai zurfi kan kalubalen da ke ci gaba da kunno kai a kasar Libya tare da fatan samar da ingantacciyar hanyar da Afirka za ta warware matsalar rashin zaman lafiya da aka kwashe shekaru 10 ana fama a kasar ta Libya da a yanzu ta zama mafaka ga kowane nau’in makamai da mayaka na kasashen waje wadanda babban tasirinsu ke fuskantar yankunan Afirka ke fama da shi.

“ Shugabanni, Mambobi masu girma, mata da maza, ku sani ta’addancin duniya, ‘yan fashi da sauran laifuffukan kasa da kasa na ci gaba da haifar da manyan kalubale ba ga Afirka kadai ba, har ma ga zaman lafiya da tsaro a duniya. Wadannan al’amuran sun zama barazana na dindindin ga ci gaban tattalin arziki da ci gaban al’umma.

 “Nijeriya da sauran hukumomin shiyya-shiyya a Afirka da ma sauran kasashen duniya suna aiki tukuru domin tunkararwa kan wadannan barazanar da ke tattare da wanzuwar bil’adama. A garemu a Nijeriya, muna ci gaba da yin hadin gwiwa tare da bangarori daban-daban don samun galaba a kan yaki da ‘ yan ta’addar Boko Haram da sauran kungiyoyin ta’addanci da ke da alaka da su.

 “Lokacin da na karbi mulki a 2015, Boko Haram sun rike kusan kashi biyu bisa uku na Jihar Borno, rabin Jihar Yobe, da kuma wasu kananan hukumomi biyu a Jihar Adamawa, duk a Arewa maso Gabashin Nijeriya. Mun samu damar dawo da wadannan yankuna ta hanyar zuba jarin sama da Dala biliyan 1 don samun makamai masu linzami daga Amurka da sauran kasashen kawayenmu don gudanar da ayyukan ci gaba da yaki da ta’addanci tun daga 2015.

A nasa jawabin, Shugaban Dandalin Wanzar da Zaman Lafiya a Tsakanin Al’ummar Musulmi, Shaykh Abdallah Bin Bayyah, ya bayyana taken taron na 2023 cewa dogara ne da shawarwarin “Sanarwar Nouakchott” da ke da nufin rushe tushen addini na maganganun masu tsattsauran ra’ayi da kuma takaita tashin hankali bisa dalilai na addini da aka sanya a matsayin takardar bayani a cikin ra’ayin zaman lafiya na Afirka a taron kolin shugabannin kasashen kungiyar Tarayyar Afirka karo na 33.

Da yake maraba da shugabanni da masana na Afirka wajen taron zaman lafiya, shugaban kasar Mauritaniya ya ce an ba shugaba Buhari lambar yabon ne saboda samar da shugabanci nagari da kuma samar da zaman lafiya a kasa mai kabilu da al’adu da harsuna da dama kamar Nijeriya, tare da kara gogewa da hikimarsa zuwa sauran kasashen Afirka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaBuhariMakamai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Wadda Za Ta Samar Da Karin Damamaki Ga Duk Duniya Aminiya Ce Ta Kasashe Masu Tasowa Har Abada

Next Post

’Yar Kasuwa Elizabeth Homes: Labarin Tashe Da Rushewarta (I)

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

6 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

8 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

13 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

13 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

17 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

1 day ago
Next Post
’Yar Kasuwa Elizabeth Homes: Labarin Tashe Da Rushewarta (I)

’Yar Kasuwa Elizabeth Homes: Labarin Tashe Da Rushewarta (I)

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.