ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

by Leadership Hausa
4 years ago
Jihohi

A bayyana yake cewa a halin yanzu Nijeriya na fadi tashi a neman samar da ci gaba a bangarori da dama, tun daga bunkasar tattalin arzki zuwa samar da ingantaciyar rayuywa ga al’umma, ana fuskantar matsaloli da dama da suke kawo wa Nijeriya cikas a kokarinta na neman ci gaba.

Amma tabbas akwai hanyoyin da suka kamata Nijeriya ta bi wajen samun mafita tare da maganin wadannan matsalolin, sun kuma hada da sanya ido da kuma karfafa mahukunta na jihohi don su tabbatar da gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon amana, hakanan a tabbatar da matakin kananan hukumomi na yin aiki yadda ya kamata, musamman ganin sune a kusa da al’umma.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • Me Sin Ta Kawo wa Duniya Cikin Shekaru 3 Da Ta Shafe Tana Kokarin Tinkarar Cutar COVID-19

Daya daga cikin manyan matsalolin da ake fuskanta a Nijeriya shi ne na rashin kyakkyawar gwamnati a matakin jihohi, jihohi da dama sun zama dandalin cin hanci da rashawa suna gudanar da ayyukansu a kudundune wanda hakan yana shafar kokarin cigaba a fadin kasar nan. In har ana son Nijeriya ta samu ci gaban da ya kamata dole a sa ido a yadda Jihohi suke gudanar da ayyukansu tare da hukunta jami’an da aka tabbatar sun aikata ba daidai ba a dukkan matakan tafiyar da harkokin jihar.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin hanyoyin tabbatar da ganin haka shi ne karfarfawa jami’an gwamnatin gwiwa jihohi su gudanar da harkokin mulki a bayyane ba tare da boye-boye ba. Za kuma a iya cimma wannan manufar ta hanyar yin amfani da dokar bayyana ayyukan gwamnati a kuma ba al’umma damar sanin dukkan yadda gwamnatin ke gudanar da ayyukanta don kowa ya sani.

Haka nan za a iya cimma wannan maufan ne ta hanyar amfani da fasahar bibiyar yadda ake aiwatar da kasafin kudi, ta haka ne al’umma za su iya sani tare da bibiyar yadda ake kashe kudadensu, suna kuma iya kama duk wani jami’in gwamnatin da ya kauce hanya ko kuma ya yi halin bera.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Yana da matukar muhimmanci a karfafa al’umma su shigo don su sani tare da bibiyar yadda ake sarrafa dukiyar gwamnatocinsu. Wannan kuma za a cimma masa ne ta hanyar samar da kungiyoyin matasa ‘yan fafutuka a tarukan da suke yi na kungiyoyin za su rinka fadakar da al’umma halin da ake ciki don suna da hakkin sanin yadda ake sarrafa dukiyoyinsu.

In aka ba al’umma damar sanya baki a kan yadda ake gudanar da harkokin gwamnatin jihohinsu, hakan zai tabbatar da gwamnati na gudaar da ayyukan da suka shafi rayuwar al’ummar ne wanda hakan kuma yana matukar muhimmanci a fagen bunkasar rayuwar al’umma a bangaren tattalin arziki dana zamantakewar kasar baki daya.

Wasu hanyoyin da za a karfafa samar da ci gaba a matakin jihohin Nijeriya sun kuma hada da zuba jari a bangaren gine-gine na da matukar muhimmanci a hanyar tabbatar da ci gaba kowanne iri saboda shine ginshikin tabbatar da bunkasar tattalin arziki. Zuba jari wajen gina abubuwa kamar su hanyoyi gadoji tashashoshin jiragen ruwa ta haka kuma za a samar da ayyukan yi ga dimbin matasanmu wanda hakan zai kai ga bunkasar tattalin arzik zai kuma kai ga daga darajar rayuwar al’ummar kasa.

Amma kuma yana da matukar muhimmanci a tabbatar da an yi ingantattun ayyuka wadanda za su amfanar da al’umma, musamman ganin a lokutta da dama ana samun sakaci da rashin sanin yakamata wajen gudanar da ayyukan ci gaba a jihohin kasar nan.

Ta hanyar tabbatar da ana gudanar da ingantattun ayyuka a matakin jihohi, Nijeriya za ta samu tabbacin jihohi suna bayar da gudummawarsu wajen bunkasar kasar gaba daya.

Akwai kuma wasu hanyaoyin na daban inda  Nijeriya za ta bayar da karfi in har ana son a tabbatar da ci gaba mai dorewa a matakin jihohin kasar nan. Misali ana iya karfafa bangaren ilimi ta yadda za a fito da hanyoyin da za a bunkasa ilijkin al’umma musamman samar da cikakkne horas da matasa sana’o’in dogaro da kai don da ilimi ne kasashe ke samun bunkasar tattalin arzik a fadin duniya.

Za kuma a iya mayar da hankali a kan karfafrawa tare da bayar da tallafin da ya kamata ga kananan masa’ana’antu musamman wadanda Suke bayar da gudummawar tabbatar da ci gaban tattalin arziki.

A bayyane lamarin yake cewa, a kwai gaggarumin aiki a gaban Nijeriya a kokrinta na wanzar da ci gaba a matakin jihohi.

Amma in har aka samar da yanayin da za a rike sanya ido akan yadda jihohin ke gudanar da ayyukansu to lallai Nijeriya ta dauki matakin samar da ci gaban da ake bukata a kasar baki daya a yanzu da kuma nan gaba.

A ra’ayinmu, wannan ne lokacin da ya dace na aiwatar da wannan matakan musamman ganin muna dunfarar babban zaben kasa.

Abin takaci a nan shi ne yawancin ‘yan Nijeriya sun mayar da hankalinsu ne a kan abin da ke faruwa a matakin gwamnatin tarayya sun manta da abin da ke faruwa a matakin gwamnatocin Jihohi da sauran matakan gwamnati.

Muna iya cewa, kyakyawar gwamnati ta mutu a matakin jihohi da kanana hukumomi. Kwanakin baya ne hukumar kididdiga ta kasa ta bayar da rahotannin tsananin talaucin da ake fama da shi a Nijeriya, in da aka bayyana cewa, kashi 63 na ‘yan Nijeriya na fama da talauci, ko kuma a ce ‘yan Nijeriya Miliyan 133 ke fama da talauci, wannan yana nuna sakaci da rashin iya aiki na gwamnati. Amma kuma abin takaicin shi ne al’umma sun fi dora alhaki a kan gwamnatin tarayya kuma in aka lura lafin duk da hannu sauran matakan gwamnati.

Nijeriya za ta iya samun cikakken ci gaba ne in aka tabbatar da wakilci daidai  a dukkan matakan gwamnati, shugaban kasab ba zai iya yin komai da komai ba dukk da irin fatansa na alhairi.

A kan haka muke kira ga masu zabe sun zabi ‘yan siyasa masu mutunci da za su iya yin aikin da ya kamatra a dukka matakai musamman a matakin jihohi. Ta haka ne Nijeriya za ta samu bunkasa zuwa matakin da dukkan mu muke mafarki kuma muke bukata.

Jihohi
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.