ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

by Alhaji Adamu Rabiu
12 months ago
WAEC

Bayan shekaru 73 da kafuwarta, Majalisar gudanar da Jarrabawar Afirka ta Yamma na bukatar yi mata garanbawul cikin gaggawa. Matsalolin da dalibai suka fuskanta a wasu cibiyoyi a lokacin jarrabawar kammala sakandare ta 2024/25 na nuni da koma bayan da WAEC ke fuskanta da kuma bukatar a yi mata kwaskwarima ga ayyukanta.

Biyo bayan fitowar takardar tambayar harshen turanci kwanaki hudu kacal kafin a fara jarrabawar, majalisar ta tilasta sake buga tambayoyin. Hakan ya sa dalibai suka zauna jarabawar har cikin dare. Lokacin da fitilun suka mutu, dalibai sun koma amfani da tocila, kyandir, da kowace irin fitila a madadin hasken lantarki. A wata cibiya wani rufi ya kusa fadowa kan wasu daga cikin zaliban.

  • Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

Lamarin dai ya jefa firgici a gidaje da dama, inda iyayen da masu kulawa suka fusata suka yi ta kiraye-kirayen kare lafiyarsu da kuma inda ‘yan uwansu suke. Rahotanni sun ce wasu jami’an hukumar ta WAEC na karkashin ‘yansanda suna binciken lamarin, wanda ya shafi cibiyoyi a Legas, Ogun, Osun, da Taraba.

ADVERTISEMENT

An kafa WAEC ne a shekarar 1952 don gudanar da jarrabawar a Nijeriya da wasu kasashe hudu na yammacin Afirka da ke magana da Ingilishi, Ghana, Saliyo, Laberiya, da Gambiya, tare da ba da izinin bayar da takaddun shaida kwatankwacin daidaikun hukumomin da ke yin jarrabawar a duniya.

Hukumar ta taka rawa daidai da yadda da ake tsammani shekaru kusan ashirin bayan kirkirar ta. Jarrabawar ta zarce yadda aka yi zato, domin na gyara rayuwar miliyoyin dalibai da suka zama kwararru, shugabannin kasa, da manyan abin alfahari a duniya a fagage daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Duk da haka, a cikin ‘yan shekarun da suka wuce, rashin daidaituwa na jiki ya bayyana. Jami’ai sun fara fitar da takardun tambayoyi domin samun kudi a wasu kwanaki kafin a fara jarabawar, inda ‘yan kasuwa marasa kishi, dillalai, da malalata dalibai suka lalata shirin.

Wannan ya gurgunta kyawawan manufofin WAEC da ta bada fatawa da kuma kawo cikas ga ingancin takaddun shaida.

Abubuwan da suka faru na baya-bayan nan sun kara jaddada lalacewar tsarin ilimin kasar. Kusan wata guda da fitowar WASSCE, matsalar tsara JAMB ta tilasta wa dubban daliban UTME a jihohi shida da wasu sassan Legas yin jarrabawar bayan an basu maki kadan.

Wannan abin takaici ya sa wata daliba da abin ya shafa ta kashe kanta a Legas, sai dai daga baya hukumar ta JAMB ta yarda cewa babbar matsalar da aka samu gazawarta ce ba ta dalibai ba.

Shekarar 1970 ta kawo sauyi a koma bayan WAEC. Badakalar Owosho, inda wani jami’in hukumar ya fallasa amsar da dalibai suka yi a gaban jarrabawar, ya sa aka soke jarabawar a wasu cibiyoyi, wanda ya tilasta wa wadanda suka yi laifi da wadanda ba su ji ba gani ba su ci jarrabawar a shekara mai zuwa tare da kananan yaransu. Sai dai, sulhun da aka yi a shekarar 1977, wanda aka yi wa lakabi da ‘Edpo’ 77’, ya rufe rugujewar Owosho ta kowace fuska.

Dole ne WAEC ta fanshi kanta ta hanyar toshe madogarar da ma’aikatan da ba su da gaskiya suke ba da takardar tambayar ta. Dole ne ta gano tare da mika miyagu ga ‘yansanda domin gurfanar da su gaban kuliya.

WAEC
Alhaji Adamu Rabiu
+ postsBio
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Rashin Tsaro A Nijeriya: Gazawar Masu Mulki Ce Da Cin Amanar Ƙasa
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • Alhaji Adamu Rabiu
    https://hausa.leadership.ng/author/alhaji-adamu-rabiu/
    Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

MASU ALAKA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Next Post
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.