• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Na Ci Gaba Da Tsare Bawa Bayan Shafe Mako 1 A Hannunsu

by Sadiq
2 years ago
DSS

Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Abdulrasheed Bawa, yana hannun jami’an tsaro na farin kaya (DSS) mako guda bayan dakatar da shi.

Ko da yake har yanzu jami’an ‘yansandan sirri ba su yi wani bayani ba a kan tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, an samu labarin cewa ana ci gaba da tuhumar Bawa kan rawar da ya taka wajen sake fasalin kudin kasar nan.

  • Sin Ta Yi Kira Da A Goyi Bayan CAR A Yunkurinta Na Shimfida Zaman Lafiya
  • RMAFC Ta Musanta Rahotonnin Karin Albashi Ga Masu Rike Da Mukaman Siyasa

Wata majiya ta ce akwai wasu batutuwan da ake tuhumarsa amma rawar da ya taka a cikin matsalar kudi a watan Fabrairun ya wuce batunsa.

Idan dai za a iya tunawa, nan take jami’an SSS suka dauke shi jim kadan bayan dakatar da shi da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi masa.

A halin da ake ciki, masu rajin kare hakkin bil’adama da kungiyoyin farar hula, sun nuna rashin amincewa da ci gaba da tsare tsohon shugaban hukumar EFCC, inda suka yi kira ga ‘yansandan sirri da su gurfanar da shi a kotu ko kuma a sake shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Salihu Aliyu, ya ce, “Ya kamata hukumar SSS ta gaggauta bincikar wadannan mutane, ina nufin Bawa da (Godwin) Emefiele, musamman (Bawa), ta gurfanar da su a kotu, ba mu ma san laifinsa ba!”

Kokarin jin martani a hukumance daga bakin kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya, ya ci tura yayin da ya ki kiran wayarsa.

Har yanzu bai mayar da martani kan sakon da aka aike masa ba har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai
Labarai

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

October 26, 2025
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Nada Manyann Mukaman Gwamnati A Jihar

Gwamnan Sakkwato Ya Nada Manyann Mukaman Gwamnati A Jihar

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

October 26, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.