ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

by Abubakar Abba
1 year ago
Dabobbi

Wasu kwararru a fannin kiwon dabbobi, sun yi kira ga Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dobbobi ta Kasa, da ta kafa cibiyoyin da za a rika gudanar da bincike, kan nau’ikan dabbobin cikin gida a shiyoyi shida na fadin kasar nan.

Sun yi kiran ne, a karkashin kungiyar masu kiwon dabbobi ta kasa (NSAP).

  • APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?
  • Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kiran nasu, sun yi shi ne a taron kungiyar karo na 50 na kasa da ya gudana a Jami’ar Tarayya da ke a garin Lafia, ta Jihar Nasarawa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, kungiyar ta yi nuni da cewa; akwai bukatar a rika taimaka wa cibiyoyin da ke gudanar da bincike kan dabbobi, musamman ta hanyar gudanar da yin bita a kai-a kai da tarurruka, wanda kuma za a rika gudanar da tarukan tare da masu bincike kan fannin dabbobi da masu samar da tsare-tsare.

Shugaban Jami’ar ta tarayya da ke garin Lafia, a Jihar Nasarawa Farfesa Shehu Abdul Rahman ne, ya bude taron.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Taken taron shi ne: “Bunkasa Fannin Kiwon Dabbobi, Domin Samar Da Wadataccen Abinci Da Bunkasa Tattalin Arzikin Kasa”.

A cikin sanarwar bayan taron da Shugaban Kungiyar Farfesa Olaniyi Babayemi da kuma Sakatarenta, Dakta Folasade Jemiseye suka sanya wa hanu, sun jaddada bukatar da a rungumi yin kiwon dabbobi ta fasahar zamani, domin a rika samar da nau’ikan dabbobin da ake kiwatawa a fadin wannan kasa.

A cewar sanarwar, akwai kuma bukatar a samar da tsarin kula da dabbobin da yadda za a rika ciyar da su da kuma sanya ido a kansu, domin kare su daga kamuwa da cututtuka.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, akwai kuma bukatar a samar da dabbobin da ke iya jurewa sauyin yanayi, sannan kuma mahukunta su kara bai wa masu kiwon dabbobin kwarin guiwa, a kan mayar da hankali domin yin kiwo tare da samar wa da masu kiwon ingantattun kayan aiki, kuma na zamani.

“Akwai bukatar masu ruwa da tsaki a fannin kiwon a kasar nan, su karfafa wa matasa guiwa, wajen rungumar yin kiwo domin samun riba da kuma samar musu da kwarewa da kuma ba su horo, wanda hakan zai sanya a cimma burin da kasar ta sanya a gaba na kara habaka fannin kiwo a kasar”, in ji sanarwar.

Dabobbi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Dabobbi

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Dabobbi

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.