• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Gargadi ‘Yan Siyasa Da Yada Labaran Karya

by Sadiq
3 years ago
DSS

Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), ta gargadi ‘yan siyasa da su kauce wa yin kalamai marasa tushe yayin da ake kusantar zaben shugaban kasa.

Wannan na zuwa ne bayan da daraktan yakin neman zaben jam’iyyar APC, Femi Fani-Kayode, ya zargi sojoji da dan takarar shugaban kasa na PDP da yunkurin yin juyin mulki.

  • ‘Yan Jihar Bauchi Sun Yabawa Buhari Kan Amincewa Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsohuwar 200
  • Baragurbin Ma’aikatan Banki Suka Jefa Talakawa Cikin Ƙunci – Buhari

DSS ta ce ya zama wajibi jam’iyyun siyasa da masu kula da kafofin yada labaransu su kaurace wa yada labaran karya a lokacin yakin neman zabe da kuma lokacin isar da sakonsu ga magoya bayansu.

DSS ta ce irin wadannan bayanan marasa tushe na iya janyo martani mai zafi da kuma tada zaune tsaye.

Gargadin na zuwa ne biyo bayan binciken da hukumar ta yi wa daya daga cikin daraktocin yakin neman zaben jam’iyyar APC mai mulki Femi Fani-Kayode.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

A shafin Twitter Fani-Kayode ya yi zargin cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar da jami’an tsaro na shirin yin juyin mulki.

Hukumar ta yi wa Fani-Kayode tambayoyi ranar Laraba, sai dai nan take Muryar Amurka ba ta ji daga hukumar ta DSS ba na game da binciken.

Paul James, jami’in sa ido a harkar zabe na kungiyar YIAGA Africa mai zaman kanta, ya ce yin kalaman batanci a tsakanin jam’iyyun siyasa ba sabon abu bane.

“Hukumar DSS na binciken batun kuma ta kira Fani-Kayode don yi masa tambayoyi, mun zuba ido mu ga yadda zata kaya. Daga zaben jihar Ondo na shekarar 2020, mun ga abubuwa kamar haka. Sojoji suka fito karara suka musanta batun.

Amma akwai bukatar a fara yin abubuwan da zasu kawo kwarin gwiwa,” a cewar James a lokacin da ya zanta da wakilin Muryar Amurka Timothy Obiezu.

Yanzu a duk mako Fani-Kayode zai bayyana gaban hukumar DSS har sai an kammala bincike.

A ranar Litinin, ya yi magana da manema labarai a Abuja bayan da ya sha tambayoyi tsawon sa’o’i biyar, inda ya ce ya yi nadamar rubuta sakon a shafin Twitter ba tare da tabbatar da sahihancin batun ba daga hukumomi.

Najeriya na fuskantar karuwar yaduwar labaran karya gabanin babban zaben da za a yi ranar 25 ga watan Fabrairu, lokacin da kasar za ta kada kuri’a domin zaben sabon shugaban kasa, inda ‘yan takara uku ke kan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Next Post
NECO Ta Fitar Da Sakamakon Jarrabawar Watan Nuwamban 2022

NECO Ta Fitar Da Sakamakon Jarrabawar Watan Nuwamban 2022

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.