• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Gargadi ‘Yan Siyasa Da Yada Labaran Karya

by Sadiq
3 years ago
DSS

Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), ta gargadi ‘yan siyasa da su kauce wa yin kalamai marasa tushe yayin da ake kusantar zaben shugaban kasa.

Wannan na zuwa ne bayan da daraktan yakin neman zaben jam’iyyar APC, Femi Fani-Kayode, ya zargi sojoji da dan takarar shugaban kasa na PDP da yunkurin yin juyin mulki.

  • ‘Yan Jihar Bauchi Sun Yabawa Buhari Kan Amincewa Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsohuwar 200
  • Baragurbin Ma’aikatan Banki Suka Jefa Talakawa Cikin Ƙunci – Buhari

DSS ta ce ya zama wajibi jam’iyyun siyasa da masu kula da kafofin yada labaransu su kaurace wa yada labaran karya a lokacin yakin neman zabe da kuma lokacin isar da sakonsu ga magoya bayansu.

DSS ta ce irin wadannan bayanan marasa tushe na iya janyo martani mai zafi da kuma tada zaune tsaye.

Gargadin na zuwa ne biyo bayan binciken da hukumar ta yi wa daya daga cikin daraktocin yakin neman zaben jam’iyyar APC mai mulki Femi Fani-Kayode.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

A shafin Twitter Fani-Kayode ya yi zargin cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar da jami’an tsaro na shirin yin juyin mulki.

Hukumar ta yi wa Fani-Kayode tambayoyi ranar Laraba, sai dai nan take Muryar Amurka ba ta ji daga hukumar ta DSS ba na game da binciken.

Paul James, jami’in sa ido a harkar zabe na kungiyar YIAGA Africa mai zaman kanta, ya ce yin kalaman batanci a tsakanin jam’iyyun siyasa ba sabon abu bane.

“Hukumar DSS na binciken batun kuma ta kira Fani-Kayode don yi masa tambayoyi, mun zuba ido mu ga yadda zata kaya. Daga zaben jihar Ondo na shekarar 2020, mun ga abubuwa kamar haka. Sojoji suka fito karara suka musanta batun.

Amma akwai bukatar a fara yin abubuwan da zasu kawo kwarin gwiwa,” a cewar James a lokacin da ya zanta da wakilin Muryar Amurka Timothy Obiezu.

Yanzu a duk mako Fani-Kayode zai bayyana gaban hukumar DSS har sai an kammala bincike.

A ranar Litinin, ya yi magana da manema labarai a Abuja bayan da ya sha tambayoyi tsawon sa’o’i biyar, inda ya ce ya yi nadamar rubuta sakon a shafin Twitter ba tare da tabbatar da sahihancin batun ba daga hukumomi.

Najeriya na fuskantar karuwar yaduwar labaran karya gabanin babban zaben da za a yi ranar 25 ga watan Fabrairu, lokacin da kasar za ta kada kuri’a domin zaben sabon shugaban kasa, inda ‘yan takara uku ke kan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Next Post
NECO Ta Fitar Da Sakamakon Jarrabawar Watan Nuwamban 2022

NECO Ta Fitar Da Sakamakon Jarrabawar Watan Nuwamban 2022

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.