• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Siyasa
0
Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwagwarmaya, jajircewa, rashin tsoro, duk wasu kalmomi ne da ake amfani dasu ne wajen yin bayani kan al’amarin daya shafi ganin sai an samu cimma wata manufa, gwagwarmayar ta siyasa sai an samu mai jajircewa ba tare da nuna tsoro ba domin kuwa idan aka fara yin ta akwai manyan matsalolin da mai da’awar kokarin yin hakan zai iya fuskanta cikin fafutukar ko gwagwarmayar da yake yi.

Ida ana maganar gwagwarmayar a duniya gaba daya ba za a taba mantawa da gudunmawar da marigayi Mista Mahatma Gandhi na Indiya,Zulfikhar Ali Bhutto, Benezir Bhutto Pakistan, Aung Suu Kyi ta kasar Myanmar, marigayi Dakta Kwame Nkurmah na Ghana, sai kuma nan gida Nijeriya ba zamu manta da wadanda suka yi gwagwamayar samun ‘yancin Nijeriya ba,domin sai kana da cikakken ‘yanci ne zaka samu damar yin harkokin siyasa ba tare da tsangwama ba.

  • Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje

Mutane kamar su sir Abubakar Tafawa Balewa,Dakta Nmadi Azikiwe,Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato K.O Mbadwe,Chief Obafemi Owolwo,Malam Aminu Kano, da  dai sauransu wadanda suka riga mu gidan gaskiya sai mu ce Allah ya jikansu ya rahamshe su.

Idan aka fara da Mahatma Gandhi jagoran siyasa na kasar Indiya ba a mantawa da irin gwagwarmayar da ya sha yi da Turawan mulkin mallaka wajen tabbatar da siyasar yadda ta kamata a kasar,ya sha wahalar gaske a hannun ‘yan mulkin mallaka nau’i daban- daban.Da haka ne har  abin ya  kai ga ‘yarsa Mrs Indira Gandhi  ta gaje shi inda ta  ci gaba daga wurin da mahaifinta ya tsaya, sannu a hankali har abin ya zo ya jikansa wato Mista Rajib Gandhi.

Idan kuma aka kalli kasar Pakistan kuma ana iya tunawa da su iyalan Bhutto kamar mulkin ya zama  masu wata baiwa ce daga Allah.Dama su kasashen Indiya da Pakistan wadannda a shekaru masu yawa da suka gabata ana kiran kasar da sunan Indo- Pakisatan daga baya ne aka raba su a shekarar 1947, kowar ce daga cikinsu ta fara cin guminta. Zulfikar Ali Bhutto Lauya ne wanda ya taba Shugabantar kasar Pakistan ta mukamin  Shugaban kasa da Firayim Ministan kasar har sau biyu daga 1971 zuwa 1973,sai kuma 1973 zuwa 1977 irin salon mulkin siyasa na kasashen Ingila  da Amurka,sai ‘yarsa Benazir Bhutto  ita ma ‘yar siiyasa ce matuka ta,Shugabanci kasar ta hanyar mukamin Firayim Minista ta 11,13, da 14,daga shekarun 1988 zuwa 1990,sai 1990 zuwa 1993, daganan sai 1993 zuwa 1996, daga karshe dai an yi mata kisan gilla ne. Aung San Suu Kyi ta kasar Myamar ‘yar gwagwamayar siyasa da kare hakkin dan Adam ta taba yin Shugabancin kasar Myamar,sanin kowa ne suna zaman manja da doya ne da hukumomin sojan kasar,an sha aikata gidan Fursunan kasar domin a halin da ake cikin yanzu tana gidan Kurkukun da zata share har shekara biyar,ba domin komai ba sai domin kare al’ummar kasar ta da take yi da kishinsu.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Marigayi tsohon Shugaban kasar Ghana Dakta Kwame Nkurmah daga shekarar1960 zuwa 1966,ya mutu ranar 27 Afrilu 1972 shine dan gwagwarmayar siyasa ne shi ma dan kishin kasa ne wanda yayi matukar suna ciki da wajen kasar Ghana

A kasar Nijeriya bayan da ‘yan kishin kasa suka yib ta fafutuka da gwagwarmayar samun ‘yancin kai,bayan an samu ‘yancin a shekarar 1960 dama an fara siyasa a karkashin kulawarTurawan mulkin mallaka na Ingila, akwai jam’iyyu da suka hada da NPC, NEPU, NCNC,da AG ko kuma jam’iyyar mutanen Arewa (Northern People Congress NPC) jam’iyyar matasan Arewa (Northern Element Progressibe Union NEPU) (National Council for Nigeria And Cameroun NCNC) ta al’umma kudu maso gabashin Nijeriya ce wato Ibo yayinda ita kuma (Action Group AG)ta al’ummar sashen Kudu maso yammcin Nijeriya ko Yarabawa.

Haka aka  fara dama Furar a lokacin aka kuma ci gaba da shan ta hakanan sai dai kuma wani al’amari daban ‘yan jam’iyyar NEPU a lokacin wadda daga baya ta koma PRP kamar su marigayi Alhaji Wada Nas,Alhaji Musa Musawa, Alhaji Sa’adu Zungur,Khalifa Hassan Yusuf,da dai sauran manyan ‘ya’yan jam’iyyar sun sha gwgwarmayar  siyasa wajen nemar maTalakawa ‘yancin kansu.

Alhaji Wada Nas Funtuwa a wata hirar da kafar yada labarai ta taba yi da shi ya ce yana taba tafiya kan Keke daga Funtuwa zuwa Kano saboda duk a cikin gwagwarmayar,madugun jam’iyyar ceton al’umma marigayi Malam Aminu Kano ya sha bakar azaba saboda akidarsa ta ganin suma Talakawa an basu dama suna bara gyada domin ai suna da Kunba.

Duk ta sanadiyar gwgwarmayar siyasa da aka yi babban zabe na shekarar1979 lokacin Nijeriya na da Jihohin goma sha tara jam’iyyar PRP a lokacin ta samu nasarar lashe zaben gwamnoni biyu daga cikin 19 ta samu Jihohin Kano da Kaduna ko shakka babu Jihohin biyu na da muhimmanci a siyasar Nijeriya,da farko dai Kaduna ita ce fadar Arewa daga cikin tane aka kirkiro Jihohi 18 na Arewa dalilin da yasa take da 19 ke nan a yanzu.

Allah ya jikansu da rahama yasa sun huta Alhaji Abdulkadir Balarabe Musa da Alhaji Abubakar Rimi sun bada gaggarumar gudunmawa wajen ci gaban Jihohin musamman ma Muhammed Abubakar Rimi da aka fi sani da Limanin canji ya ci gaba daga inada marigayi  Abdu Bako ya tsaya wanda ya fara  dora tubalin bunkasar Jihar Kano.Shi marigayi  Alhaji Abdulkadir Ballarabe Musa zamanin da yayi mulkin Jihar Kaduna bai samu damar mulki kamar yadda yake so ba a dalilin takin – sakar da ya rika yi da ‘yan majalisar Jihar Kaduna wadanda yawancinsu ‘yan jam’iyyar NPC a karkashin jagoranci Mamman Abubakar Danmusa wanda a lokacin shine Kakain majalisar Jihar.Daga karshe dai  sai da suka tsige shi daga mukamin gwmanan Jihar.

Wani abinda ba za a taba mantawa da shi ba Jihohin biyu shine yadda gwamnonin biyu suka bada dokar hana biyan Haraji da Jangali,wanda sanin kowa ne sanadiyar biyan Haraji da Jangali Talakawan Arewa da yawa daga cikinsu sun bar garuruwansu domin lokacin Sarakunan gargajiya na Arewacin Nijeriya suna da matukar karfin mulkin sun gallazawa Talakawa matuka suka hana su sakat sanadiyar biyan Haraji da Jangali yayin da shi Haraji duk Talakawa na biya shi kuwa Jangali mafi yawa Fulani suke biya na Dabbobinsu,janye maganar biyan nau’oin Harajin ba karamin taimakawa Talakawa yayi ba.

Da haka ne abu na ta tafiya wato gwagwarmayar siyasa domin wasu su masu sa’ida har abin ya zo ga madugu uban tafiya Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya nuna a salon tafiyar da mulkinsa,yayi koyi da gwarazan manya wadanda suka kwanta dama sun yi gwagwarmayar siyasa da a lokacin tafi wadda yake yi yanzu wuya.Lokacin da ya zama gwamnan Jihar Kano da Sanata ya taimakawa Talakawa da da’yansu musamman ma ta bangaren ilmiin da ya tura wasu zuwa kasashen wajen suka yi karatu sun dawo gida Nijeriya sun zama wasu suna bada tasu gudunmawar.

Har ya zuwa lokacin daya  fara neman takarar Shugaban kasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar APC da aka yi Kwankwanso ya zo na uku,amma daga karshe ya sake komawa jam’iyyar PDP wanda har zuwa lokacin da aka yi babban zabe na 2019 yana da dan takarar gwamna na Jihar Kano Injiya Abba Kabir Yusuf da aka fi sani  da Gida- gida.A zaben an yi gwagwagwa da gwagwarmaya tunda bayan zabe an fara bayyana sakamako na kananan hukumomi inda jam’iyyar PDP k e gaba, sai daga baya al’amarin ya zama da ba a kammala ba da ake ce ma inconclusibe.

Hausawa sun ce asha ruwa a koma aiki haka Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ci gaba da yi domin kuwa bayan ya sake fita daga jam’iyyar PDP ya kafa jam’iyyar siyasa har wasu nayi ma shi kallon ba zai iya zuwa ko ina ba,amma cikin ikon Allah Abba Gida—gida ya sake tsayawa takarar gwamna a karkashin jam’iyyar shi kuma ya tsaya takarar Shugaban kasa.

Bayan zaben Shugaban kasa dana ‘yan majalisun kasa jam’iyyar tana da Sanatoci 2 da ‘yan majalisar kasa 18, shi kuma ya samu nasarar lashe kuri’un Jihar Kano da gaggarumin rinjaye na fiye da 900,000,a zaben gwamnan da aka yi Asabar 18 Maris 2023 bayan da aka bayyana sakamako Injiniya Abba Kabir ya lashe zaben Jihar da kuri’u fiye da milyan daya abin ya zama conclusibe da aka kammala.Mahakurci watarana mawadaci ne kamar yadda masu iya magana suka cewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwagwarmayaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Next Post

A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d

Related

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

17 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

21 hours ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

2 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

2 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

4 days ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

6 days ago
Next Post
A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d

A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.