• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da karuwar darajar naira, tsadar farashin kayayyaki ta ci gaba da lulawa sama a Nijeriya. A yanzu dai ana sayar da kowacce dalar Amurka guda daya kan naira 1 a kasuwannin bayan fage.

A cewar hukumomi, wannan matakin ci gaba ne kuma tagomashi ne da naira ke samu a kan dala, sai dai duk da wannan matakin, tsadar kayan masarufi bai ragu ba, illa ma karuwa da ya yi.

  • Jihar Benuwai Ta Bankado Mutum 35 Masu Yi Wa Sirin Tattara Harajinta Zagon-Kasa
  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar kiddiga ta kasa (NBS) ta ce farashin kayan masarufi ya sake yin tashin gwauron zabi da kaso 33.20 a cikin 100 a watan Maris din 2024, idan aka kwatanta da kaso 31.70 cikin 100 a watan Fabrairu.

Ci gaban tagomashin da aka samu a kan darajar naira kan dalar Amurka ya samu ne tun a ranar 26 ga watan Satumban 2023.

A cikin shekara guda an samu karuwar hauhawar farashi da kaso 11.16, idan aka kwatanta da kaso 22.04 cikin dari a watan Maris din 2023.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

A cewar rahoton, tashin farashin kayan abinci ya haura da kaso 40.01 a cikin shekara guda a watan Maris, sama da kaso 15.56 cikin dari da aka samu kari domin a watan Maris na 2023 farashin na kaso 24.45.

Kayan da suka tashin sun hada da na farashin makamashi zuwa kaso 25.90 cikin dari a watan Maris, inda ya karu da kaso 6.26 sabanin kaso 19.63 da aka samu a watan Maris na 2023.

Hukumar NBS ta ce tashin farashin kayan abinci ya samu asali ne sakamakon karuwar farashin gari, gero buredi da nau’ikan hatsi, doya, dawa, da kuma busasshen kifi.

Sauran abubuwan da suka janyo tashin farashin kayan abincin sun kuma kunshi mangyade, nama, hanta, madara, bombita, ruwan lelon da dai sauransu.

Bugu da kari, tsadar kudin sufuri da zirga-zirga su ma sun kara ba da gudunmawa wajen tashin farashin kayan masarufi a Nijeriya, kamar yadda rahoton hukumar NBS ta tabbatar.

Tambayen da Nijeriya suke ci gaba da yi shi ne, me ya sa farashin kayayyaki ba su sauko kasa ba? Domin a baya ana cewa tashin farashin dala ne ya haifar da tsadar kayayyaki.

Wasu daga cikin ‘yan kasuwa sun bayyana cewa saukar farashin dal aba zai iya sauko da farashin kayayyaki nan take ba, domin mafi yawancinsu suna tare da tsofaffin kayayyaki ne wanda suka siyo a lokacin tsadar farashin dala, sai sun iya sayar da wadannan kayayyaki ne kafin za su sayo sabbin kaya a farashi mai rahusa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci – Marafan Gonin Gora

Related

Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

1 hour ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

2 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

3 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

6 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

6 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci – Marafan Gonin Gora

Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci - Marafan Gonin Gora

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.