• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu
3 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi ya fuskanci matsaloli da dama watanni bakwai bayan hukuncin kotun koli.

Lauyoyi sun bayyana damuwarsu kan yadda aka jinkinta aiwatar da hukuncin kotun koli, wanda suka nuna cewa ba a mutunta hukuncin kotun kolin tare da nuna yadda gwamnatin Nijeriya ke yawan kauce wa hukuncin shari’a.

  • An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta ba da umarnin cewa dole ne a biya su kason kananan hukumomi kasonsu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, kamar yadda babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi, SAN, ya bukata a karar da ya shigar a gaban kotun koli.

Fagbemi dai ya shigar da karar ne a madadin gwamnatin tarayya, inda ya nemi a ba da cikakken ‘yancin cin gashin kai da samar da kudade kai tsaye ga daukacin kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Ya bukaci kotun kolin da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnonin jihohi ba tare da bin doka ba su rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

Sai dai gwamnatocin jihohi 36, ta hannun lauyoyinsu, sun shigar da kara a gaban kotun, inda suka ce kotun koli ba ta da hurumin sauraren karar.

Sun kuma kulubalanci babban lauyan gwamnatin tarayya cewa bai da hurumin kai karar a madadin kananan hukumomin.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin asa.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar nan.

“Akwai bukatar yin adalci domin ci gaba da dorewar doka. Matsayin wannan kotun shi ne, gwamnatin tarayya ta iya biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ba hannun jihohi ba.

“A wannan yanayin, tun da biyan kudi ta hanyar jihohi bai yi aiki ba, bisa adalcin wannan kotu, ta zartar da hukunci cewa a biya kananan hukumomi kasonsu daga asusun tarayya kai tsaye,” in ji kotun.

Kotun koli ta kara ba da umarnin hana wadanda ake tuhuma da wakilansu ko kuma ba su kariya daga kashe kudaden kananan hukumomi. Ta kuma bayyana cewa ka da wata gwamnatin jiha ta karbi kudaden kananan hukumomi.

Bugu da kari, kotun ta ce gwamnatocin jihohi ba su da ikon nada kwamitocin rikon kwarya kuma kananan hukumomin da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya ne kadai doka ta amincewa da su.

Haka kuma, kotun kolin ta umurci gwamnatin tarayya da ta zartar da wannan hukuncin cikin gaggawa.

Sai dai, maimakon zartar hukuncin kotun koli cikin gaggawa, gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi danwaken zagaye da hukuncin da kuma kokarin kaucewa aiwatar da shi.

Lauyoyin sun nuna damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ke kin aiwatar da hukuncin kotun koli wajen zubar da mutuncin ikon bangaren shari’a.

Kotun koli ita ce ke da hurumin yanke hukunci na karshe, kuma hukuncin ya shafi dukkan kananan kotuna da wadanda abin ya shafa, kamar yadda sashe na 233 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada.

Rahotanni sun bayyana cewa yunkurin farko na kawo cikas ga aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi shi ne, na dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi wa gwamnoni na tsawon watanni uku a watan Agustan 2024.

Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun amince da dakatarwar ne a kan matsalolin da ke tattare da tasirinsa wajen biyan albashi, yadda ake gudanar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YanciHukunciKotuƘananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano

Next Post

Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

Related

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 day ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 day ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
Kotun
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
Next Post
Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

Yanzu Yanzu - Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.