• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi ya fuskanci matsaloli da dama watanni bakwai bayan hukuncin kotun koli.

Lauyoyi sun bayyana damuwarsu kan yadda aka jinkinta aiwatar da hukuncin kotun koli, wanda suka nuna cewa ba a mutunta hukuncin kotun kolin tare da nuna yadda gwamnatin Nijeriya ke yawan kauce wa hukuncin shari’a.

  • An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta ba da umarnin cewa dole ne a biya su kason kananan hukumomi kasonsu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, kamar yadda babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi, SAN, ya bukata a karar da ya shigar a gaban kotun koli.

Fagbemi dai ya shigar da karar ne a madadin gwamnatin tarayya, inda ya nemi a ba da cikakken ‘yancin cin gashin kai da samar da kudade kai tsaye ga daukacin kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Ya bukaci kotun kolin da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnonin jihohi ba tare da bin doka ba su rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Sai dai gwamnatocin jihohi 36, ta hannun lauyoyinsu, sun shigar da kara a gaban kotun, inda suka ce kotun koli ba ta da hurumin sauraren karar.

Sun kuma kulubalanci babban lauyan gwamnatin tarayya cewa bai da hurumin kai karar a madadin kananan hukumomin.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin asa.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar nan.

“Akwai bukatar yin adalci domin ci gaba da dorewar doka. Matsayin wannan kotun shi ne, gwamnatin tarayya ta iya biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ba hannun jihohi ba.

“A wannan yanayin, tun da biyan kudi ta hanyar jihohi bai yi aiki ba, bisa adalcin wannan kotu, ta zartar da hukunci cewa a biya kananan hukumomi kasonsu daga asusun tarayya kai tsaye,” in ji kotun.

Kotun koli ta kara ba da umarnin hana wadanda ake tuhuma da wakilansu ko kuma ba su kariya daga kashe kudaden kananan hukumomi. Ta kuma bayyana cewa ka da wata gwamnatin jiha ta karbi kudaden kananan hukumomi.

Bugu da kari, kotun ta ce gwamnatocin jihohi ba su da ikon nada kwamitocin rikon kwarya kuma kananan hukumomin da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya ne kadai doka ta amincewa da su.

Haka kuma, kotun kolin ta umurci gwamnatin tarayya da ta zartar da wannan hukuncin cikin gaggawa.

Sai dai, maimakon zartar hukuncin kotun koli cikin gaggawa, gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi danwaken zagaye da hukuncin da kuma kokarin kaucewa aiwatar da shi.

Lauyoyin sun nuna damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ke kin aiwatar da hukuncin kotun koli wajen zubar da mutuncin ikon bangaren shari’a.

Kotun koli ita ce ke da hurumin yanke hukunci na karshe, kuma hukuncin ya shafi dukkan kananan kotuna da wadanda abin ya shafa, kamar yadda sashe na 233 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada.

Rahotanni sun bayyana cewa yunkurin farko na kawo cikas ga aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi shi ne, na dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi wa gwamnoni na tsawon watanni uku a watan Agustan 2024.

Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun amince da dakatarwar ne a kan matsalolin da ke tattare da tasirinsa wajen biyan albashi, yadda ake gudanar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YanciHukunciKotuƘananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano

Next Post

Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

7 days ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

7 days ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

3 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

4 weeks ago
Next Post
Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

Yanzu Yanzu - Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

LABARAI MASU NASABA

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

June 20, 2025
Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

June 20, 2025
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

June 20, 2025
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

June 20, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

June 20, 2025
Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

June 20, 2025
Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

June 20, 2025
Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

June 20, 2025
Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

June 20, 2025
An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.