ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kotun

Aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi ya fuskanci matsaloli da dama watanni bakwai bayan hukuncin kotun koli.

Lauyoyi sun bayyana damuwarsu kan yadda aka jinkinta aiwatar da hukuncin kotun koli, wanda suka nuna cewa ba a mutunta hukuncin kotun kolin tare da nuna yadda gwamnatin Nijeriya ke yawan kauce wa hukuncin shari’a.

  • An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta ba da umarnin cewa dole ne a biya su kason kananan hukumomi kasonsu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, kamar yadda babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi, SAN, ya bukata a karar da ya shigar a gaban kotun koli.

ADVERTISEMENT

Fagbemi dai ya shigar da karar ne a madadin gwamnatin tarayya, inda ya nemi a ba da cikakken ‘yancin cin gashin kai da samar da kudade kai tsaye ga daukacin kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Ya bukaci kotun kolin da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnonin jihohi ba tare da bin doka ba su rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Sai dai gwamnatocin jihohi 36, ta hannun lauyoyinsu, sun shigar da kara a gaban kotun, inda suka ce kotun koli ba ta da hurumin sauraren karar.

Sun kuma kulubalanci babban lauyan gwamnatin tarayya cewa bai da hurumin kai karar a madadin kananan hukumomin.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin asa.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar nan.

“Akwai bukatar yin adalci domin ci gaba da dorewar doka. Matsayin wannan kotun shi ne, gwamnatin tarayya ta iya biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ba hannun jihohi ba.

“A wannan yanayin, tun da biyan kudi ta hanyar jihohi bai yi aiki ba, bisa adalcin wannan kotu, ta zartar da hukunci cewa a biya kananan hukumomi kasonsu daga asusun tarayya kai tsaye,” in ji kotun.

Kotun koli ta kara ba da umarnin hana wadanda ake tuhuma da wakilansu ko kuma ba su kariya daga kashe kudaden kananan hukumomi. Ta kuma bayyana cewa ka da wata gwamnatin jiha ta karbi kudaden kananan hukumomi.

Bugu da kari, kotun ta ce gwamnatocin jihohi ba su da ikon nada kwamitocin rikon kwarya kuma kananan hukumomin da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya ne kadai doka ta amincewa da su.

Haka kuma, kotun kolin ta umurci gwamnatin tarayya da ta zartar da wannan hukuncin cikin gaggawa.

Sai dai, maimakon zartar hukuncin kotun koli cikin gaggawa, gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi danwaken zagaye da hukuncin da kuma kokarin kaucewa aiwatar da shi.

Lauyoyin sun nuna damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ke kin aiwatar da hukuncin kotun koli wajen zubar da mutuncin ikon bangaren shari’a.

Kotun koli ita ce ke da hurumin yanke hukunci na karshe, kuma hukuncin ya shafi dukkan kananan kotuna da wadanda abin ya shafa, kamar yadda sashe na 233 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada.

Rahotanni sun bayyana cewa yunkurin farko na kawo cikas ga aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi shi ne, na dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi wa gwamnoni na tsawon watanni uku a watan Agustan 2024.

Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun amince da dakatarwar ne a kan matsalolin da ke tattare da tasirinsa wajen biyan albashi, yadda ake gudanar

Kotun
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

Yanzu Yanzu - Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.