ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Kotun

Aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi ya fuskanci matsaloli da dama watanni bakwai bayan hukuncin kotun koli.

Lauyoyi sun bayyana damuwarsu kan yadda aka jinkinta aiwatar da hukuncin kotun koli, wanda suka nuna cewa ba a mutunta hukuncin kotun kolin tare da nuna yadda gwamnatin Nijeriya ke yawan kauce wa hukuncin shari’a.

  • An Bude Cibiyar Tattarawa Da Yada Labarai Ta Taruka Biyu Na Sin
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta ba da umarnin cewa dole ne a biya su kason kananan hukumomi kasonsu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya, kamar yadda babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi, SAN, ya bukata a karar da ya shigar a gaban kotun koli.

ADVERTISEMENT

Fagbemi dai ya shigar da karar ne a madadin gwamnatin tarayya, inda ya nemi a ba da cikakken ‘yancin cin gashin kai da samar da kudade kai tsaye ga daukacin kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Ya bukaci kotun kolin da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnonin jihohi ba tare da bin doka ba su rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Sai dai gwamnatocin jihohi 36, ta hannun lauyoyinsu, sun shigar da kara a gaban kotun, inda suka ce kotun koli ba ta da hurumin sauraren karar.

Sun kuma kulubalanci babban lauyan gwamnatin tarayya cewa bai da hurumin kai karar a madadin kananan hukumomin.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin asa.

Duk da haka, kotun kolin ta tabbatar da huruminta. A wani hukunci da mai shari’a Emmanuel Agim ya karanta, kotun ta ce ci gaba da rike kudaden kananan hukumomi ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar nan.

“Akwai bukatar yin adalci domin ci gaba da dorewar doka. Matsayin wannan kotun shi ne, gwamnatin tarayya ta iya biyan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ba hannun jihohi ba.

“A wannan yanayin, tun da biyan kudi ta hanyar jihohi bai yi aiki ba, bisa adalcin wannan kotu, ta zartar da hukunci cewa a biya kananan hukumomi kasonsu daga asusun tarayya kai tsaye,” in ji kotun.

Kotun koli ta kara ba da umarnin hana wadanda ake tuhuma da wakilansu ko kuma ba su kariya daga kashe kudaden kananan hukumomi. Ta kuma bayyana cewa ka da wata gwamnatin jiha ta karbi kudaden kananan hukumomi.

Bugu da kari, kotun ta ce gwamnatocin jihohi ba su da ikon nada kwamitocin rikon kwarya kuma kananan hukumomin da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya ne kadai doka ta amincewa da su.

Haka kuma, kotun kolin ta umurci gwamnatin tarayya da ta zartar da wannan hukuncin cikin gaggawa.

Sai dai, maimakon zartar hukuncin kotun koli cikin gaggawa, gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi danwaken zagaye da hukuncin da kuma kokarin kaucewa aiwatar da shi.

Lauyoyin sun nuna damuwarsu kan yadda gwamnatin tarayya ke kin aiwatar da hukuncin kotun koli wajen zubar da mutuncin ikon bangaren shari’a.

Kotun koli ita ce ke da hurumin yanke hukunci na karshe, kuma hukuncin ya shafi dukkan kananan kotuna da wadanda abin ya shafa, kamar yadda sashe na 233 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada.

Rahotanni sun bayyana cewa yunkurin farko na kawo cikas ga aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi shi ne, na dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi wa gwamnoni na tsawon watanni uku a watan Agustan 2024.

Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun amince da dakatarwar ne a kan matsalolin da ke tattare da tasirinsa wajen biyan albashi, yadda ake gudanar

Kotun
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

Yanzu Yanzu - Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.