ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Zabe

Kotun Ƙoli ta bayyana cewa zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a Jihar Rivers a ranar 5 ga Oktoba, 2024, ba shi da inganci, kuma ya saɓa wa doka. Kotun ta yanke hukuncin cewa zaɓen ya kasance haramtacce, kuma saboda rashin bin ƙa’idojin da doka ta tanada kafin gudanar da irin wannan zaɓe.

A cewar kotun, hukumar zabte ta Jihar Rivers (RSIEC) ta karya dokokin gudanar da zabe, inda ta saɓa wa sashi na 150 na dokar zaɓe ta 2022.

A baya dai, wata babbar kotu a Abuja ta hana hukumar zabe ta ƙasa (INEC) bayar da rajistar masu kaɗa ƙuri’a ga RSIEC domin gudanar da zaɓen, bisa hujjar cewa ba a cika sharuɗɗan gudanar da zaɓe ba. Haka kuma, kotun ta hana Sufeto Janar na ‘Yansanda da hukumar tsaro ta DSS samar da tsaro yayin zaɓen, domin gujewa duk wata matsala da ka iya tasowa. Wannan umarni ya biyo bayan ƙarar da jam’iyyar APC ta shigar, tare da rakiyar lauyoyinta Joseph Daudu, Sebastine Hon, da Ogwu James Onoja, dukkaninsu SAN.

ADVERTISEMENT
  • Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas
  • Jam’iyyar APC Ta Sahalewa Shugaba Tinubu Damar Neman Shugabancin Nijeriya A 2027

Kotun ta bayyana cewa RSIEC ta yi kuskure wajen sanya ranar zaɓe ba tare da bin dokokin da suka wajaba ba, ciki har da rashin sanar da jama’a kwanaki 90 kafin a gudanar da zaɓen, kamar yadda doka ta tanada. Haka kuma, an gaza sabunta da tantance rajistar masu kaɗa kuri’a, wanda hakan ya saɓa wa ƙa’idar zaɓe. Saboda haka, kotun ta ayyana cewa zaben bai cika ƙa’idojin doka ba, kuma ba za a amince da sakamakonsa ba.

Bugu da ƙari, kotun ta haramta amfani da rajistar masu kaɗa ƙuri’a da INEC ta tanadar, har sai an cika dukkan sharuddan da doka ta tanada. Wannan hukunci na kotu yana nufin cewa duk wanda aka zaɓa a ƙarƙashin wannan zaɓe ba zai ci gaba da riƙe muƙaminsa ba.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Wannan mataki yana da matuƙar tasiri a siyasar Jihar Ribas, inda jam’iyyar APP ce ta lashe mafi yawan kujeru a zaɓen da aka soke.

Zabe
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post

Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa - Gwamnatin Kano Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.