• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

by Sani Anwar and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni na bayyana cewa, ‘yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare tare da kashe mutane da kuma sace dabbobi da dukiyoyin al’umma a wasu sassa na yankin Karamar Hukumar Shinkafi da ke Jihar Zamfara.

A kusa-kusan nan, ‘yan bindiga sun kashe akalla mutum biyar tare da raunata wasu mutum hudu a garin Galadi da ke karamar hukumar.

  • NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

Wadannan hare-hare, na ci gaba da afkuwa duk kuwa da yunkurin yin sulhu da al’ummomin wasu garuruwa na Karamar Hukumar Shinkafin da ake yi da ‘yan bindigan da kuma matakan tsaro iri daban-daban da ake ci gaba da dauka.

Har ila yau, wannan atsala ta hare-haren ‘yan bindiga da ta zame wa yankin Arewa Maso Yamma tamkar wani karfen-kafa, na ci gaba da addabar garin Galadi da sauran kauyuka da dama da ke makwabtaka da shi a yankin Karamar Hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara. Kamar dai yadda wani mutumin yankin ya laburta.

“Wadannan ‘yan bindiga, sun kawo hari wani gari da ke kusa da mu mai suna Bargaja a ranar Litinin da ta gabata da rana tsaka, inda suka dauki mutane suna tsaka da aiki a cikin gonakinsu.

Labarai Masu Nasaba

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

“Haka nan, ‘yan bindigan, suna sake kawo wani harin a wannan gari namu na Galadi da misalign karfe 10:15 na daren ranar Laraba, inda suka kewaye baki-dayan Galadin; illa bangare guda shi ma saboda gulbi ya tare wannan gefen ne, inda suka bude wa Galadin wuta ta kowane gefe baki-daya,” in ji shi.

Kazalika ya kara da cewa, “Babu shakka, wannan hari ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane biyar, inda kuma wasu hudu ke kwance a gadon asibiti. Sai dai, Allah cikin ikonsa ya sa ba su samu damar tafiya da ko mutum guda ba,sakamakon dauki da aka samu daga wasu jami’an tsaro da suka garzayo daga Shinkafi.

“Duk da cewa, a nan muna da jami’an tsaro; amma a lokacin da suka kawo wannan hari, sai da suka mamaye sansanin jami’an tsaron baki-daya,” kamar yadda ya bayyana.

Har wa yau, wannan Bawan Allah da ke wannan yanki na Galadi da ya nemi a sakaya sunansa ya kara da cewa; wadannan hare-hare na ci gaba da afkuwa, duk kuwa da shirin da al’ummomin yankin ke yi da kuma na gwamnatin tarayya, na tattaunawar sulhu da ‘yan bindigan.

Yayin da aka tuntubi babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Zamfara kan kafafen yada labarai, Mustafa Jafaru Kaura cewa ya yi; har yanzu matsayin gwamnatin jihar bai sauya ba game da kaucewa tattaunawa ko yin sulhu da ‘yan bindiga.

“Saboda haka, koda wani abu ya faru a wannan gari na Galadi, ko shakka babu, Gwamnatin Jihar Zamfara na matukar bakin ciki da faruwar al’amari, sannan kuma tana yin iya kokarinta wajen ganin an ci gaba da fatattakar wadannan barayi, don ganin Allah ya kawo mana saukin al’amarin.”

Bugu da kari, masana harkokin tsaro na ci gaba da yin tsokacin cewa; kokarin magance matsalar ta tsaro a yankin Arewa Maso Yammacin Nijeriya , abu ne da ke bukatar matakai irin na bai- daya.

Sannan kuma, wajibi ne a wadanda za a dauka a dauke su a lokaci guda, idan dai har ana so a ga karshen wannan matsala da ta ki ci ta ki cinyewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Next Post

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Related

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

27 minutes ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

2 hours ago
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira
Manyan Labarai

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

3 hours ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

5 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

6 hours ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

7 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Hadin Tsumin Baure

Hadin Tsumin Baure

September 27, 2025
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

September 27, 2025
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

September 27, 2025
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

September 27, 2025
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

September 27, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

September 27, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.