ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

by Sani Anwar and Sulaiman
10 months ago
Bindiga

Rahotanni na bayyana cewa, ‘yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare tare da kashe mutane da kuma sace dabbobi da dukiyoyin al’umma a wasu sassa na yankin Karamar Hukumar Shinkafi da ke Jihar Zamfara.

A kusa-kusan nan, ‘yan bindiga sun kashe akalla mutum biyar tare da raunata wasu mutum hudu a garin Galadi da ke karamar hukumar.

  • NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

Wadannan hare-hare, na ci gaba da afkuwa duk kuwa da yunkurin yin sulhu da al’ummomin wasu garuruwa na Karamar Hukumar Shinkafin da ake yi da ‘yan bindigan da kuma matakan tsaro iri daban-daban da ake ci gaba da dauka.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, wannan atsala ta hare-haren ‘yan bindiga da ta zame wa yankin Arewa Maso Yamma tamkar wani karfen-kafa, na ci gaba da addabar garin Galadi da sauran kauyuka da dama da ke makwabtaka da shi a yankin Karamar Hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara. Kamar dai yadda wani mutumin yankin ya laburta.

“Wadannan ‘yan bindiga, sun kawo hari wani gari da ke kusa da mu mai suna Bargaja a ranar Litinin da ta gabata da rana tsaka, inda suka dauki mutane suna tsaka da aiki a cikin gonakinsu.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

“Haka nan, ‘yan bindigan, suna sake kawo wani harin a wannan gari namu na Galadi da misalign karfe 10:15 na daren ranar Laraba, inda suka kewaye baki-dayan Galadin; illa bangare guda shi ma saboda gulbi ya tare wannan gefen ne, inda suka bude wa Galadin wuta ta kowane gefe baki-daya,” in ji shi.

Kazalika ya kara da cewa, “Babu shakka, wannan hari ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane biyar, inda kuma wasu hudu ke kwance a gadon asibiti. Sai dai, Allah cikin ikonsa ya sa ba su samu damar tafiya da ko mutum guda ba,sakamakon dauki da aka samu daga wasu jami’an tsaro da suka garzayo daga Shinkafi.

“Duk da cewa, a nan muna da jami’an tsaro; amma a lokacin da suka kawo wannan hari, sai da suka mamaye sansanin jami’an tsaron baki-daya,” kamar yadda ya bayyana.

Har wa yau, wannan Bawan Allah da ke wannan yanki na Galadi da ya nemi a sakaya sunansa ya kara da cewa; wadannan hare-hare na ci gaba da afkuwa, duk kuwa da shirin da al’ummomin yankin ke yi da kuma na gwamnatin tarayya, na tattaunawar sulhu da ‘yan bindigan.

Yayin da aka tuntubi babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Zamfara kan kafafen yada labarai, Mustafa Jafaru Kaura cewa ya yi; har yanzu matsayin gwamnatin jihar bai sauya ba game da kaucewa tattaunawa ko yin sulhu da ‘yan bindiga.

“Saboda haka, koda wani abu ya faru a wannan gari na Galadi, ko shakka babu, Gwamnatin Jihar Zamfara na matukar bakin ciki da faruwar al’amari, sannan kuma tana yin iya kokarinta wajen ganin an ci gaba da fatattakar wadannan barayi, don ganin Allah ya kawo mana saukin al’amarin.”

Bugu da kari, masana harkokin tsaro na ci gaba da yin tsokacin cewa; kokarin magance matsalar ta tsaro a yankin Arewa Maso Yammacin Nijeriya , abu ne da ke bukatar matakai irin na bai- daya.

Sannan kuma, wajibi ne a wadanda za a dauka a dauke su a lokaci guda, idan dai har ana so a ga karshen wannan matsala da ta ki ci ta ki cinyewa.

Bindiga
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Bindiga
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

MASU ALAKA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.