Shahararriyar jaruma a Masana’antar Kannywood, wadda ta yi shura a masana’antar; Nafisa Abdullahi ta bayyana cewa, akwai buƙatar duk wanda zai zama miji a gare ta; ya fara sanin wace ce ita? don gujewa abin da ka je ya dawo.
Jarumar, ta yi tashe matuƙa cikin ƙanƙanin lokaci; sakamakon yadda take sakin jiki ta yi rawa a duk lokacin da ta samu kanta a shirin fim.
- Masu Sha’awar Shiga Harkar Fim Su Shiga Da Zuciya Daya -Auwal Marafa
- Rahoto Ya Nuna Yadda Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Ke Tafiya Cikin Tagomashi
A wani shiri da aka tattaunawa da Nafisan ta bayyana cewa, akwai buƙatar iyaye su fahimci cewa; tarbiyyar yara ya kansu ba kawai a bar uwa da xawainiyar tarbiyyar yaran kaxai ba, sannan kamata ya yi uba ya xauki kashi 50 na tarbiyyar yaransa; haka nan ita ma uwa ta xauki kashi 50.
Har ila yau, jarumar wadda ta fito a manyan fina-finan Hausa a Arewa da kuma na Kudancin wannan ƙasa ta bayyana cewa, duk da wasu na kallon ta a matsayin wata abar koyi a wajensu, amma fa hakan ba zai tilasta mata riƙa yin abin da lallai sai ya burge su ba.
“Kasancewata abar koyi a wajen waxansu mutane, musamman mata; ba zai zai sa na tauye kaina wajen riƙa yin abin da ba shi ne ra’ayina ba, domin kuwa ni ba ni da wani wanda nake kallo a matsayin abin kwaikwayo a wajena; don haka ni ban tilasta wa kowa yin koyi da ni ba, kowa ya je ya yi nasa ra’ayin”.
Har ila yau, ta ƙara da cewa; “Rayuwa sauƙi ne da ita, sannan kuma al’ada na iya canzawa a kowane lokaci, xan’adam kuma tara yake bai cika goma ba; wani lokaci zai iya yin daidai, wani lokaci kuma ya yi kuskure. Saboda haka, idan na ce kowane lokaci a yi koyi da abin da nake yi; akwai yiwuwar wasu su tsinci kansu wajen aikata ba daidai ba, wanda ni kuma ba zan so hakan ba”, in ji Nafisa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp