• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Wanda Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani, Shi Ma Sai An Hukunta Shi – Gwamna Sule 

bySulaiman
8 months ago
Sule

Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya sha alwashin zakulo duk wadanda suke da hannu a rikincin da ya barke a garin Mararraba Udege da kauyen Oduh a makon da ya gabata.

 

Ya ce, “hakkin Gwamnati ne ta samar da zaman lafiya da kare dukiyoyin al’umma, don haka, duk wanda aka samu da hannu a wannan rikicin za a mika shi gaban kotu ta yi masa hukunci daidai da abinda ya aikata.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Baƙin Haure 165, An Miƙa Wa Hukumar NIS A Kebbi
  • Kuɗin Fansa ₦13m, Kasonsa ₦200,000: Ɗan Shekara 50 Ya Jagoranci Garkuwa Da Ɗansa Da Iyalansa 

“Abin bakin ciki ne mutanen da suke ‘yan kabila daya, Asali daya, Uwa daya, Uba daya amma suna kashe junansu saboda son zuciya da kwadayin abin Duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Wannan jahilci ne, babu yadda mai hankali zai yarda ya kashe dan uwanshi saboda abin duniya.

 

“Babu wata kabila da ake kira Afon dutsi ko Afon kasa. Duk sunansu AFO.  Ya kuma janyo hankalin matasa da su daina yarda ‘yan siyasa batagari na amfani da su wajen neman biyan bukatar kansu, suna sanya su kashe junansu ko kona gidajen al’umma.”

 

Gwamna Abdullahi Sule ya kara da cewa, ya je kasar Sin don tattaunawa da kamfanin hakar Ma’adanai na ‘Juling Lithium Nasarawa Lithium Project’ a birnin Beijing, don ganin yadda kamfanin zai sake habaka basirar ma’aikata Leburori da ke aiki a kamfanin da ke Udege. Ganin cewa, ma’aikatan fiye da shekaru 20,  aikin leburanci kawai suke yi babu ci gaba, don haka, dole a samu sauyi.

 

“Na tattauna da manyan Shugabannin kamfanin Shneyen. Nace sama da shekara 20 kuna hakar ma’adinan Tantalaye a Udege kuna tafiya da shi. Amma mutanen Udege baya ga aikin leburanci babu wani aikin da kuka basu. saboda haka, yanzu me zaku yi Wanda matasan gurin zasu samu aikin yi? Wannan maganar ta tabasu sosai. Nan take suka ce, za su gina katafaren kamfani da za a dauki matasa aiki a koyar dasu ilimin yadda ake sarrafa Ma’adinai da sauransu.

 

“Don haka, bai dace a kawo hargitsin da zai yi sanadin kulle wannan kamfani da wannan alherin da ke shirin zuwa wannan yankin ba, saboda banbancin siyasa.”

 

Shima a nasa jawabin OSu- Ajiris na Udege Mbeki Dr. Alhaji Halilu Bala ya yi godiya ga Gwamna Abdullahi Sule da ya yi tattaki da tawagarsa yazo ya gane wa idanunsa kuma ya dauki matakin da ya dace.

 

Sarkin yayi kira ga wadanda aka yi wa barna da su kara hakuri, doka za ta yi aiki kan duk wanda aka kama da hannu kan tayar da rikicin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version