• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Wanda Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani, Shi Ma Sai An Hukunta Shi – Gwamna Sule 

by Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
Duk Wanda Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani, Shi Ma Sai An Hukunta Shi – Gwamna Sule 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya sha alwashin zakulo duk wadanda suke da hannu a rikincin da ya barke a garin Mararraba Udege da kauyen Oduh a makon da ya gabata.

 

Ya ce, “hakkin Gwamnati ne ta samar da zaman lafiya da kare dukiyoyin al’umma, don haka, duk wanda aka samu da hannu a wannan rikicin za a mika shi gaban kotu ta yi masa hukunci daidai da abinda ya aikata.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Baƙin Haure 165, An Miƙa Wa Hukumar NIS A Kebbi
  • Kuɗin Fansa ₦13m, Kasonsa ₦200,000: Ɗan Shekara 50 Ya Jagoranci Garkuwa Da Ɗansa Da Iyalansa 

“Abin bakin ciki ne mutanen da suke ‘yan kabila daya, Asali daya, Uwa daya, Uba daya amma suna kashe junansu saboda son zuciya da kwadayin abin Duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

“Wannan jahilci ne, babu yadda mai hankali zai yarda ya kashe dan uwanshi saboda abin duniya.

 

“Babu wata kabila da ake kira Afon dutsi ko Afon kasa. Duk sunansu AFO.  Ya kuma janyo hankalin matasa da su daina yarda ‘yan siyasa batagari na amfani da su wajen neman biyan bukatar kansu, suna sanya su kashe junansu ko kona gidajen al’umma.”

 

Gwamna Abdullahi Sule ya kara da cewa, ya je kasar Sin don tattaunawa da kamfanin hakar Ma’adanai na ‘Juling Lithium Nasarawa Lithium Project’ a birnin Beijing, don ganin yadda kamfanin zai sake habaka basirar ma’aikata Leburori da ke aiki a kamfanin da ke Udege. Ganin cewa, ma’aikatan fiye da shekaru 20,  aikin leburanci kawai suke yi babu ci gaba, don haka, dole a samu sauyi.

 

“Na tattauna da manyan Shugabannin kamfanin Shneyen. Nace sama da shekara 20 kuna hakar ma’adinan Tantalaye a Udege kuna tafiya da shi. Amma mutanen Udege baya ga aikin leburanci babu wani aikin da kuka basu. saboda haka, yanzu me zaku yi Wanda matasan gurin zasu samu aikin yi? Wannan maganar ta tabasu sosai. Nan take suka ce, za su gina katafaren kamfani da za a dauki matasa aiki a koyar dasu ilimin yadda ake sarrafa Ma’adinai da sauransu.

 

“Don haka, bai dace a kawo hargitsin da zai yi sanadin kulle wannan kamfani da wannan alherin da ke shirin zuwa wannan yankin ba, saboda banbancin siyasa.”

 

Shima a nasa jawabin OSu- Ajiris na Udege Mbeki Dr. Alhaji Halilu Bala ya yi godiya ga Gwamna Abdullahi Sule da ya yi tattaki da tawagarsa yazo ya gane wa idanunsa kuma ya dauki matakin da ya dace.

 

Sarkin yayi kira ga wadanda aka yi wa barna da su kara hakuri, doka za ta yi aiki kan duk wanda aka kama da hannu kan tayar da rikicin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Baƙin Haure 165, An Miƙa Wa Hukumar NIS A Kebbi

Next Post

Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

7 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

9 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

10 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

11 hours ago
Next Post
Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.